Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ƙasarsa ta ƙaddamar da hare-haren soji kan mayaƙan ƙungiyar ISIS (Daesh) a Arewa Maso Yammacin Nijeriya, yana mai cewa hare-haren sun biyo bayan zargin kashe-kashen fararen hula, musamman Kiristoci, da ƙungiyar ke yi tsawon shekaru.
A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social ranar Alhamis, Trump ya ce hare-haren sun gudana ne da dare bisa umarninsa a matsayinsa na Babban Kwamandan sojojin Amurka, inda Pentagon ta aiwatar da “gagarumin hari mai ƙarfi” da ya ce Amurka kaɗai ke da ikon kai irinsa.
Cibiyar umarnin sojojin Amurka a Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da harin a wani saƙo da ta wallafa a shafin X, inda ta ce an kai harin ne a jihar Sokoto, kuma an kashe mayaƙan ISIS da dama. AFRICOM ta ce hare-haren sun nuna ƙudurin Amurka na kawar da duk wata barazanar ta’addanci a gida da waje.
Rahotanni sun kuma nuna cewa jiragen saman leƙen asirin Amurka sun fara zirga-zirga a wasu sassan Nijeriya tun daga ƙarshen watan Nuwamba, domin tattara bayanan sirri kan ayyukan ƙungiyoyin ta’addanci.
A baya, Trump ya yi iƙirarin cewa ana kashe Kiristoci da yawa a Nijeriya, lamarin da ya sa ya umarci Pentagon da ta shirya yiwuwar kai hari. Sai dai gwamnatin Nijeriya ta musanta zarge-zargen, inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jaddada cewa gwamnatinsa na ci gaba da tattaunawa da shugabannin Kiristoci da Musulmai domin ƙarfafa zaman lafiya da magance matsalolin tsaro ba tare da nuna wariya ba.














