Afirka Duniya Ghana

Ghana ta tura injiniyoyin soji 54 zuwa Jamaica bayan mummunar guguwa

Ghana ta aike da injiniyoyin soji 54 zuwa Jamaica domin taimakawa aikin sake gina ƙasar bayan guguwar Hurricane Melissa. Matakin na nuna ƙarfafa haɗin kai tsakanin Afirka da Caribbean a lokutan bala’i.

Newstimehub

Newstimehub

18 Dec, 2025

40fb965333e991b400cb9d0185a51a84effe808cc47b6d2bccb378b174837b9e e1766249925967

Ghana ta tura injiniyoyin soji 54 zuwa Jamaica domin taimaka wa aikin sake gina ababen more rayuwa da guguwar Hurricane Melissa ta lalata. Guguwar ta kashe sama da mutum 40 tare da haddasa asarar da ta kai kusan dala biliyan 8.8, kamar yadda Ma’aikatar Harkokin Wajen Ghana ta bayyana.

Sojojin daga rundunar injiniyoyi ta 14 za su bayar da gudunmawa a fannin aikin injiniya, sake gini da jigila, yayin da Jamaica ke ƙoƙarin farfaɗo da al’ummomin da bala’in ya shafa tare da haɗin gwiwar ƙasashen duniya. Shugaba John Dramani Mahama, manyan jami’an gwamnati, kwamandojin soji, jami’an diflomasiyya da wakilan Jamaica sun halarci bikin tafiyar sojojin. Mahama ya ce wannan mataki alama ce ta goyon bayan Ghana ga Jamaica, tare da bayyana sojojin a matsayin jakadun jinƙai da ƙwarewar fasaha.

Ministan Harkokin Wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya ce manufar harkokin wajen ƙasar na ta’allaka ne kan haɗin kai da taimakon ƙasashen da ke buƙata, yana mai cewa an tura sojojin ne bisa buƙatar Firayim Ministan Jamaica, Andrew Holness. Guguwar Hurricane Melissa ta afka wa Haiti, Jamaica da Cuba a ƙarshen Oktoba, inda ta haddasa ambaliyar ruwa, zaftarewar ƙasa da asarar rayuka. Zuwa ranar 2 ga Disamba, rahotanni sun nuna cewa guguwar ta kashe mutane 88, ciki har da aƙalla 45 a Jamaica da 43 a Haiti.

Majiyar Labari: Trt Hausa