Ajanda

Kotu Ta Kwace Gidaje 57 Na Malami Masu Darajar ₦213.2bn a Wucin Gadi

Kotun Tarayya ta kwace kadarori 57 masu darajar ₦213.2bn da ake alakantawa da Malami a wucin gadi tare da bai wa masu ruwa da tsaki kwanaki 14 su bayyana hujjoji.

Newstimehub

Newstimehub

7 Jan, 2026

Abubakar Malami e1767813923691

Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin wucin gadi na kwace kadarori guda 57 da ake dangantawa da tsohon Ministan Shari’a na Tarayyar Najeriya, Abubakar Malami (SAN), tare da wasu ‘ya’yansa biyu.

Kotun ta bayyana cewa kadarorin, wadanda kimar su ta kai ₦213,234,120,000, ana zargin an samo su ne ta hanyar da ba ta dace ba, kuma suna cikin Abuja, Kebbi, Kano da Kaduna. Mai shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da wannan umarni bayan wani ƙarar gaggawa da Lauyan EFCC, SAN Ekele Iheanacho, ya shigar a gaban kotu.

A cikin hukuncinsa, mai shari’ar ya ce kadarorin za a mika su na wucin gadi ga Gwamnatin Tarayya, tare da bayar da umarni a wallafa sanarwar a jarida domin ba duk wanda ke da bukatar su damar bayyana hujja cikin kwanaki 14. An dage shari’ar zuwa 27 ga Janairu, 2026 domin ci gaba da sauraro da kuma bayar da rahoton bin umarni. A halin yanzu, Malami, matarsa da ɗansa na fuskantar shari’ar zargin halatta kuɗin haramun da yawansu ya kai ₦8.7bn a gaban kotun.

Majiyar Labari: Channels News