Rundunar sojin Nijeriya ta ɗauki matakin biyan diyya ga iyalan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon harin sama da ya afku a jihar Sokoto. Rundunar Sojin Saman Nijeriya (NAF) ta ce diyyar ta shafi dangogin waɗanda harin kuskure na sojin ya rutsa da su a ranar 25 ga Disamban 2024, a ƙauyukan Gidan Bisa da Rumtuwa da ke ƙaramar hukumar Silame.
Babban Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin, Air Vice Marshal Edward Gabkwet ne ya miƙa diyyar a madadin babban hafsan sojin saman Nijeriya, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, yayin wata ziyara da ya kai yankin. A yayin ziyarar, ya bayyana godiyarsa ga gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, bisa kyakkyawar tarba da kuma ci gaba da bayar da goyon baya da haɗin kai daga gwamnatin jihar ga rundunar sojin.
Da yake bayani kan yadda lamarin ya faru, jami’in ya ce an kai harin ne a ƙarƙashin shirin tsaro na “Fansan Yamma”, bayan samun bayanan sirri da ke nuna motsin ‘yan ta’adda a yankunan da abin ya shafa.
Sai dai bayan harin, an miƙa koke a watan Afrilun 2025, wanda ya sa aka buɗe bincike kan lamarin. Binciken ya nuna cewa fararen hula 13 sun rasa rayukansu, yayin da wasu mutum takwas suka jikkata. Jami’in sojin ya bayyana lamarin a matsayin abin baƙin ciki, tare da amincewa da kuskuren da aka yi.
A nasa jawabin, gwamnan Sokoto ya yaba wa Rundunar Sojin Saman Nijeriya bisa nuna ƙwarewa, gaskiya, da kuma tausayi wajen ɗaukar alhakin abin da ya faru, yana mai jaddada muhimmancin kare rayukan fararen hula a kowane irin aiki na tsaro.














