‘Yansandan Nijeriya 10 sun rasa rayukansu a musayar wuta da mahara a arewacin ƙasar, in ji hukumomi

Wata mummunar musayar wuta tsakanin wasu mahara da ke ɗauke da makamai da jami’an tsaron Nijeriya ta yi sanadiyyar mutuwar jami’ai 10 da mahara 17 a wani ƙauye a Masarautar Zuru a kan iyakar jihohin Kebbi da Zamfara da ke arewa maso yammacin ƙasar.
11 Aug, 2026
‘Yan Nijeriya sun kashe Naira tiriliyan 6.6 kan sayen datar waya a cikin shekara ɗaya

An ƙididdige wannan adadi ne bisa bayanan yawan amfani da intanet da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya (NCC) ta fitar, tare da amfani da matsakaicin ƙimar naira 431 kan kowane gigabyte (GB), ba wai bisa kuɗaɗen shiga da kamfanonin sadarwa suka bayyana ba.
11 Aug, 2026
Sojojin Nijeriya sun kashe Abu Khalid Al Muhajir da wasu kwamandojin ISWAP tara a Borno

Daga cikin waɗanda aka kashe har da Abu Khalid Al Muhajir, wanda aka bayyana a matsayin babban kwamandan ISWAP mai kula da samar da tawagar tsaro ta musamman da ke raka manyan jami’an ƙungiyar ta’addancin yayin zirga-zirgarsu.
10 Aug, 2026
Masarautar Kano ta musanta bidiyon da ake yadawa kan Sarki Sanusi II ya samu ‘carry-over’ a jami’a

Bidiyon, wanda ya bazu sosai a ranar Lahadi, ya yi zargin cewa tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriyar bai cika ƙa’idar cin nasarar ɗaya daga cikin darussansa ba.
10 Aug, 2026

Gwamnatin Nijeriya za ta fara sarrafa kayayyakin tsara iyali a cikin ƙasar

Hukumar EFCC ta rufe asusun gwamnatin Jihar Osun kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamna

Rundunar sojin Nijeriya ta sanya tukuicin N60m kan kwamandan ISWAP da mataimakinsa

An yi motsin ƙasa a wasu sassan Abuja

An saki gomman mutanen da aka yi garkuwa da su a Jihar Kwara bayan wata shida a hannun ‘yanta’adda
5 Aug, 2026
WAEC ta riƙe sakamakon jarrabawar ɗalibai 167,486
Ranar Laraba ne shugaban ofishin ƙasa na WAEC a Nijeriya, Dr Amos Dangut ya bayyana hakan lokacin jawabinsa yayin sakin sakamakon jarrabawa a Lagos.

5 Aug, 2026
Dakarun Nijeriya sun kama mutanen da ake zargi da kai wa ‘yan Boko Haram ƙwayoyi a Borno da Yobe
Wasu daga cikin abubuwan da aka gano sun haɗa da tabar wiwi da wayoyin hannu masu yawa da na’urar cajin waya da wukake da tocila da kwalayen sigari da kapsul na Pregabalin, maganin tari da katunan shaida da katunan banki da kuɗaɗe.

4 Aug, 2026
Gwamnati ta ba jami’o’i da kwalejojin Nijeriya umarnin korar ɗalibai da ke da alaka da satar mutane
“Idan aka daɗe ana kyale munanan ɗabi’u, suna zama al’ada. Duk ɗalibin da aka samu, bayan cikakken bincike, da laifin shirya ko shiga satar ɗalibai takwarorinsa, ba shi da gurbi a manyan makarantunmu. Dole ne a kore irin waɗannan mutane”.

4 Aug, 2026
‘Yansandan Nijeriya sun kama mutum 48 a samamen da suka kai maɓoyar masu laifi a Zamfara
A cikin wata sanarwa, Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jihar, DSP Yazid Abubakar, ya ce aikin da aka gudanar bisa sahihan bayanan sirri ya kai ga nasarar ƙwato babura 17, kekuna uku, janareta guda ɗaya, lasifikoki uku da ganguna uku.

3 Aug, 2026
An saki anƙalin da aka yi garkuwa da shi a jihar Kebbin Nijeriya
An saci Bunza ne ranar 26 ga watan Yuli a gidansa da ke kan hanyar Zogirma a Ƙaramar Hukumar Bunza ta jihar Kebbi.

3 Aug, 2026
‘Yanbindiga sun kashe mutum 12, sun yi garkuwa da mata da yara a wani ƙauyen Sokoto a Nijeriya
An ƙona mutum shida ‘yan gida ɗaya ƙurmus a harin, kamar yadda wani mazaunin yankin ga shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters.

2 Aug, 2026
Nijeriya ta tura sojoji 86 domin aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau
Tawagar wadda ta ƙunshi sojoji 86 ta tashi daga filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Asabar.

1 Aug, 2026
Sojojin Nijeriya sun daƙile yunƙurin ‘yanta’adda na garkuwa da mutane 31 a Borno
Sanarwar ta ce sojojin sun yi nasarar daƙile yunƙurin sace mutanen ne a kan hanyar Buratai zuwa Kamuya a ƙaramar hukumar Biu ta jihar Borno.

31 Jul, 2026
Remi Tinubu ta nemi Saudiyya ta tallafa wa ilimin almajirai a Nijeriya
Matar shugaban Nijeriya ta ce akwai buƙatar Nijeriya ta ƙarfafa haɗin gwiwarta da masarautar Saudiyya don gyara tsarin ilimin Almajiri ta hanyar hada karatun Musulunci da na zamani.

30 Jul, 2026
Nijeriya ta lalata makamai guda 2,819 da ta kama a matakin dakile rashin tsaro
An lalata makaman ne a daidai lokacin da Nijeriya ke fama da ‘yan bindiga, satar mutane, ta’addanci, da rikice-rikicen al’umma.



