Gwamnatin Nijeriya ta karɓo ɗalibai 100 da aka sace daga St. Mary’s Catholic School a Jihar Neja

‘Yanbindiga sun kai hari a makarantar St. Mary’s Catholic School da ke Papiri a Jihar Neja ne ranar 21 ga watan Nuwamba inda suka sace mutum 315 — ɗalibai 303 da malamai 12.
8 Dec, 2025
Tawagar Majalisar Dokokin Amurka ta isa Nijeriya, ta tattauna da Nuhu Ribadu

Babban Mai Bai wa Shugaban Nijeriya Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu ya ce tawagar ta je Nijeriya ne domin tattara bayanai bayan tattaunawar diflomasiyya da tawagar Nijeriya ta yi a Washington a kwanakin baya kan zargin tauye haƙƙin addini.
7 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya za ta fara rufe wuraren sana’ar POS marasa rajista daga Janairun 2026

Hukumar da ke yi wa Kamfanonin Rajista a Nijeriya ta yi gargaɗi game da masu gudanar da sana’ar POS ba tare da rajista ba inda ta ce daga Janairun 2026, jami’an tsaro za su fara rufe duk wani wurin sana’ar POS maras rajista.
6 Dec, 2025
Kakakin Majalisar Jihar Ribas da wasu ‘yan majalisa 16 sun sauya sheƙa daga PDP zuwa APC

Majalisar ta gudanar da zamanta a yau, inda waɗanda suka sauya sheƙar suke cewa sun bar jam’iyyar ta PDP ne saboda rikicin cikin gida da ya addabi jam’iyyar.
5 Dec, 2025

Ghana na shirin kashe dala biliyan 3.4 a fannin makamashin da ake iya sabuntawa

Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya ta amince da N100bn don gyara cibiyoyin horas da ‘yansanda

Sakataren Harkokin Wajen Amurka ya ce za a taƙaita ba da biza kan ‘muzguna wa Kiristoci a Nijeriya’

CBN ya bayyana iya abin da mutum zai iya cirewa a ATM duk sati

Shin Matsin Lambar Amurka Na Iya Zama Dalilin Tsananta Rashin Tsaro a Najeriya?
3 Dec, 2025
An sako mutanen da aka yi garkuwa da su a cocin Kwara.
An tabbatar da cewa gwamnatin jihar da hukumomin tsaro za su ci gaba da aiki tare domin tabbatar da irin wannan lamari bai sake faruwa ba.

3 Dec, 2025
Gwamnatin Kano za ta sayi jirage marasa matuƙa don magance rashin tsaro a kan iyakokin jihar
Wannan matakin ya zo ne bayan jerin hare-haren da ‘yan bindiga suka kai kwanan nan a Kananan Hukumomin Tsanyawa da Shanono.

2 Dec, 2025
Majalisar Dattawa Ta Sauya Shugabanci a Manyan Kwamitoci na Tsaro
Sauye-sauyen sun yi nufin ƙara ƙarfin Majalisar Dattawa wajen tunkarar batutuwan tsaro a duk faɗin ƙasa.

2 Dec, 2025
Majalisar Dokokin Amurka Za Ta Tattauna Tsaro a Nijeriya
Taron ya nufi duba matsalar tsaro da ‘yancin addini a Nijeriya tare da ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin Amurka da Nijeriya.

2 Dec, 2025
Tinubu ya naɗa Christopher Musa Ministan Tsaron Nijeriya
Tinubu ya bayyana haka ne a wata sanarwa da kakakinsa, Bayo Onanuga ya fitar ranar Talata.

2 Dec, 2025
Ahmed Tinubu ya naɗa tsohon hafsan saro, Janar Christopher Gwabin Musa, a matsayin sabon Ministan Tsaro na ƙasa.
Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Christopher Gwabin Musa tsohon Babban Hafsan Tsaro a matsayin sabon Ministan Tsaro a Nijeriya, ya maye gurbin Mohammed Badaru Abubakar, bayan saukar Bayan Badaru daga muƙaminsa.

2 Dec, 2025
‘Yan majalisar dokokin Amurka za su gana ranar Talata a kan ‘ta’azzarar rashin tsaro’ a Nijeriya
Taron zai kuma kunshi bayanai daga wakilan kwamitin Amurka kan ‘yancin addini na duniya da sauran kwararru kan batutuwan da suka shafi hakan.

2 Dec, 2025
Gwamnonin arewacin Nijeriya na neman a dakatar da haƙar ma’adinai domin matsalar tsaro
Gwamnonin arewacin Nijeriya, waɗanda suka sha alwashin kafa asusun tsaro na naira biliyan ɗaya, sun kuma tabbatar da goyon bayansu ga ƙoƙarin samar da tsarin ‘yan sanda na jihohi.

1 Dec, 2025
Masu kamuwa da cutar HIV sun ragu da kaso 46 cikin 100 a Nijeriya
Dakta Temitope Ilori, Darakta-Janar ta Hukumar Kula da Cutar AIDS ta Kasa (NACA), ta ce a shekarar 2024, an yi wa mata masu juna biyu fiye da miliyan biyar gwajin cutar, a yunƙurin kare jariran da za su haifa daga kamuwa da cutar.

1 Dec, 2025
Takaitaccen Labari: Barazanar da Gwamna Bago ke yi wa ‘yan jarida a Neja
Gwamna Bago na amfani da tsoro da barazana ga ‘yan jarida, inda ake kokarin dakile rahoto kan matsalolin tsaro a jihar. Gwamnati ta saba amfani da jami’an tsaro wajen cafke ko tsare ‘yan jarida, lamarin da ya kara nuna cewa tsaron jihar Neja na ci gaba da tabarbarewa. Wannan yanayi ya sa ‘yan jarida ke gudanar da aikinsu cikin fargaba da kuma tsoron rasa rayuwarsu.


