Yahudawa ‘yan-kama-wuri-zauna sun cinna wa masallatai biyu wuta a Gabar Yammacin Kogin Jordan

Majiyoyin yankin sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu cewa wasu daga cikin mazaunan matsugunan sun kutsa cikin ƙauyen Jiljilya da asubahin ranar, inda suka banka wa masallacin ƙauyen wuta.
17 Jun, 2026
Amurka da Iran sun amince su kawo ƙarshen yaƙi. Amma akwai wanda za a iya cewa ya yi nasara?

Amurka da Iran na gaf da sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da za ta kawo janye takunkumai da bude mashigar teku ta Hormuz gaba daya.
16 Jun, 2026
Trump ya sanar da cim ma yarjejeniyar Iran mai tarihi, ya yi alƙawarin buɗe Mashigar Hormuz nan-take

“Na ba da cikakkken izinin buɗe Mashigar Hormuz, haka kuma a lokaci guda, na ba da izinin janye killacewar da jiragen ruwa yaƙin Amurka suka yi nan-take,” a cewar shugaban Amurka a ranar Lahadi.
15 Jun, 2026
Yarjejeniyar Amurka da Iran ta ƙunshi sake buɗe Hormuz, taƙaita aikin nukiliya: babban jami’i a Iran

Wani babban jami’in Iran ya shaida wa Reuters cewa daftarin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka ya ƙunshi batutuwa daga shirin nukiliyar Tehran zuwa sake buɗe Mashigar Hormuz da kuma sassaucin Amurka kan takunkumin man fetur.
14 Jun, 2026

Iran za ta gudanar da jana’izar Jagoran Addini da aka kashe Ali Khamenei a ranakun 4-9 ga Yuli

An gano wani dutse mai ɗauke da rubutun sunan Khalifa Umar ibn Khattab a Madina

Iran ta kai hare-hare manyan cibiyoyin sojin Amurka 18 a Kuwait da Bahrain yayin da hankula ke tashi

Amurka ta kai hare-hare da dama ta sama Iran yayin da hankula suka tashi kan sake ɓarkewar yaƙi

Turkiyya da Saudiyya sun sa hannu kan muhimman yarjejeniyoyi a fannin layin dogo da sufuri
9 Jun, 2026
Helikwaftan sojin Amurka ya faɗi kusa da Mashigar Hormuz; matuƙansa suna ‘lafiya’, in ji Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya ce matuƙan wani jirgi suna cikin ƙoshin lafiya bayan wani jirgi mai saukar angulu na sojin Amurka ya faɗi a kusa da Mashigar ruwan Hormuz.

8 Jun, 2026
Ƙungiyar Houthi ta yi barazanar haramta wa Isra’ila jigilar kayayyaki a Bahar Rum gaba ɗaya
Kungiyar Houthi ta Yemen ta yi gargadin tsananta kai hare-haren jiragen ruwa da kuma sabbunta na makamai masu linzami, tana mai danganta matakinta da karuwar rikice-rikice a faɗin Gabas ta Tsakiya.

8 Jun, 2026
Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare a faɗin Iran yayin da yaƙin Gabas Ta Tsakiya ya sake ɓarkewa
An ba da rahotannin fashewar abubuwa a biranen Iran, ciki har da Tehran da Tabriz da Isfahan da wurare kusa da Karaj, yayin da ƙasar ke fama da sabbin jerin hare-haren Isra’ila.

5 Jun, 2026
Iraniyawa sun nuna juriya da ƙalubale irin na lokacin yaƙi a wani gagarumin gangami a Tehran
Titunan birnin Tehran sun cika maƙil da bukukuwa, inda aka jera ƙofofin balan-balan masu launuka da kayatarwa tsawon kilomitoci, tutocin Iran suna kadawa, da kuma taron jama’a masu murna — wani yanayin biki mara iyaka da ya bambanta da yanayin yaki.

3 Jun, 2026
Fashe-fashe sun girgiza tsibirin Qeshm na Iran yayin da Kuwait ta tare jerin makamai masu linzami
Kafofin watsa labaran Iran sun ba da rahoton fashewar abubuwa a bakin teku, da ake ganin makamai masu linzami ne, yayin da rundunar sojin Kuwait ta ce ƙarar fashewar abubuwa da aka ji na kakkaɓo makamai ne da tsarin tsaron sararin samaniya ya yi.

2 Jun, 2026
Iran ta ce ta kai hari kan wani jirgi mai alaƙa da Amurka da Isra’ila bayan hari kan wani jirginta
Rundunar IRGC ta yi gargaɗin cewa za ta mayar da martani kakkausa kan duk wani matakin sojin Amurka, tana mai cewa dakarun ruwanta sun ƙaddamar da “harin ramuwar gayya” kan wani jirgin ruwn da ta yi iƙirarin cewa yana da alaƙa da Amurka da Isra’ila.

1 Jun, 2026
Iran ta dakatar da tattaunawa da Amurka saboda hare-haren Isra’ila a Lebanon: rahoto
Tehran ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawa ba har sai Isra’ila ta daina kai hari a Gaza da Lebanon, kamar yadda kafafen watsa labarai na Iran suka bayyana.

1 Jun, 2026
Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka a Kuwait bayan hari kan benen sadarwar Hormozgan
Rundunar kare juyin juya hali na Iran ta yi iƙirarin cewa an lalata dukkan ababen da suka kai wa harin na ramuwar gayya kan a wani sansanin sojin Amurka a Kuwait.

1 Jun, 2026
Masar ta yi kira ga kwamitin tsaro na MƊD ta dakatar da faɗaɗa [harin] da Isra’ila ke yi a Lebanon
Masar ta yi kira ga kwamitin tsaro na Majslaisar Ɗinkin Duniya (MƊD) ta daukin matakin gaggawa domin dakatar da hare-haren sojin da Isra’ila ke yi da kuma hare-haren ƙasa da take yi a Lebanon.

31 May, 2026
Iran ta ci gaba da aikin samar da gas a wurarenta uku na South Pars da ke cikin teku
South Pars, wanda Iran ke rabawa da Qatar, shi ne wurin samar da iskar gas mafi girma a duniya, kuma yana samar da mafi yawan iskar gas ɗin da Iran ke fitarwa.



