Fiye da mutum 5000 sun tsere saboda rashin tsaro da ke daɗa ƙamari a Darfur ta Yamma a Sudan: MDD

Da yawa daga cikin iyalan da lamarin ya shafa sun kasance waɗanda aka tilasta musu barin gidajensu ne kuma suka ƙetare zuwa cikin, in ji hukumar IOM ta Majalisar Dinkin Duniya.
10 Aug, 2026
Hatsarin mota ya kashe mutum 22, ciki har da sojoji 17 a Nijar

Minsitan Sufurin ƙasar Kanal-Manjo Abdourahamane Amadou ya ce zai gayyaci kamfanonin STM da SONITRAV, waɗanda a tsakanin motocinsu ne hatsarin ya auku, su bayyana a ofishinsa ranar Litinin
9 Aug, 2026
Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta yi kira ga Chadi ta janye matakinta na ficewa daga kotun

Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta yi gargaɗin cewa ficewar na barazanar zagon ƙasa ga ƙoƙarin kawo ƙarshen rashin hukunta laifuka.
8 Aug, 2026
Guinea ta nemi Faransa ta mayar da ƙoƙon kawunan ‘yan ƙasarta masu fafutuka

Guinea na neman Faransa ta dawo da ƙoƙon kawuna da kayayyakin fitattun mutane da dama masu tarihi, waɗanda suka yi yaƙi da mulkin mallaka a ƙarni na 19.
8 Aug, 2026

Kenya na binciken abin da ake tunanin guba ce wadda ta kashe giwaye 16

Kwamitin tattaunawa na Libiya ya cim ma matsaya kan tsarin ɗaukar shugaban hukumar zaɓe

Shugaba Biya na Kamaru, wanda ba ya nan, ya yi sauye-suaye a shugabancin sojin ƙasar

Ghana ta amince da ɗaurin shekara 20 ga duk wanda ya mayar da gonar koko zuwa wani abu daban

Ɗaruruwan mutane sun yi hijira daga kudu maso yammacin Nijar saboda hare-haren ‘yanta’adda
1 Aug, 2026
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati
Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Jamhuriyar Nijar ANP bai faɗi adadin sojojin da aka kashe ba, sai dai ya tabbatar da cewa an kashe sojoji a harin da aka kai a kusa da garin N’Guigmi da ke yankin Tafkin Chadi.

31 Jul, 2026
Adadin ‘yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya
Sifaniya ta tura dakaru tare da rufe kan iyakarta a Melilla bayan an samu isowar mutane da yawa daga Maroko, yayin da Rabat ke ƙoƙarin hana ƙarin tsallakewar mutane.

31 Jul, 2026
Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa’adin mulkin shugaban ƙasa
Shawarar na daga wani ɓangare na shirin gyaran kundin tsarin mulkin Ghana.

30 Jul, 2026
Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026
A tsakiyar watan Yulin 2026, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta sanar da dakatar da bayar da biza daga birane 25 a faɗin Afirka, inda tilas masu neman bizar su tafi wasu biranen a abin da Washington ta bayyana “cibiyoyin yanki.”

28 Jul, 2026
Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa
Gwamnatin ta Nijar ta zargi dillalan da boye siminti mai yawa duk da shirin gwamnati na sayar da siminti a farashi mai rangwame domin sauƙaƙa wa jama’a samun kayan gini.

28 Jul, 2026
Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar
Akwai ‘yan Sudan fiye da 100,000 waɗanda suka amince su koma ƙasarsu bisa raɗin kansu yayin da hukumomin na Libya suka fitar da baƙin-haure 117,350 aƙalla daga ƙasar.

27 Jul, 2026
Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu
Sulemana Abdul Samed, wanda ake ganin shi ne namijin da ya fi kowa tsawo a Ghana, ya rasu yana da shekara 32, kamar yadda kafar watsa labaran ƙasar(GBC), ta ruwaito ranar Litinin.

27 Jul, 2026
Chadi ta sanar da shirin janyewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)
Daga cikin bincike 13 da kotun ta gudanar tun lokacin da ta fara aiki, tara sun shafi ƙasashen Afirka ne, yayin da huɗu kacal aka gudanar da su a sauran yankunan duniya “amma ba tare da samun wani ci-gaba na a-zo-a-gani ba,” a cewar gwamnatin Chadi.

27 Jul, 2026
An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati
Masu zanga-zangar sun yi tir da matsalar wutar lantarki, yawan katsewar ruwa, raunin tsarin kiwon lafiya da kuma hauhawar farashin kayayyaki, a cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Libya.

25 Jul, 2026
Ƙarin ma’aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000
Adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Kongo ya kai 2,973, ciki har da mutum 1,309 da suka mutu, in ji ƙididdigar da gwamnati ta fitar ranar Jumma’a a batun da hukumomi suka tabbatar cewa shi ne yaɗuwar cutar da ta fi sauri a tarihi.



