An samu akalla gawawwaki 58 da ba a tantance su ba a wani asibiti a Libya

Minsitan cikin gida na Libya ya ce an gano gawawwakin ne a wajen adana gawawwaki a wata mutuware a Asibitin Abu salim a birnin Tarabulus
20 May, 2025
Shugaban soji na Sudan, Burhan ya naɗa sabon firaministan ƙasar

Shugaban Majalisar Tsaron Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya naɗa Kamil El-Tayib Idris, wani tsohon jami’in Majalisar Dinkin Duniya, a matsayin Firaministan Sudan.
19 May, 2025
Kotun MDD za ta yanke hukunci kan rikicin Gabon da Equatorial Guinea kan yankuna masu arzikin mai

Rikicin dai ya samo asali ne tun a shekarar 1900, lokacin da ƙasashen Faransa da Sifaniya da suka yi mulkin mallaka suka rattaba hannu kan wata yarjejeniya a birnin Pariskan da nufin samar da iyakokin ƙasashen biyu.
19 May, 2025
Ɗan ƙunar-baƙin-wake ya kashe mutum 11 a Mogadishu babban birnin Somalia

Mutumin ya tayar da bam ɗin ne a daidai lokacin da wasu matasa masu neman shiga aikin soja suka yi jerin-gwano a wajen wani sansanin soji a Mogadishu.
18 May, 2025

Ghana ta kama ‘yan kasashen waje fiye da 2,000 da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba

Sojoji sun ‘ɗauke’ tsohon Firaiministan Chadi Succes Masra

Gwamnatin Nijar ta haramta achaɓa a wasu sassan yankin Dosso

Mayakan RSF sun kai harin da ya katse lantarki a Khartoum

Hajjin 2025: Jirgin farko dauke da alhazai 363 ‘yan Nijar ya tashi zuwa Saudiyya
13 May, 2025
Afirka ta Kudu za ta dukaka kara kan wanke fasto dan Nijeriya daga zargin fyade
An wanke Fasto ɗan Nijeriya, Timothy Omotoso daga zargin aikata fyaɗe bayan da mai shri’a ya gano cewa masu gabatar da ƙara sun yi kusukure wajen shigar da ƙarar.

13 May, 2025
Shugaban Ghana nemi kasashen Afirka su tsayar da manufa daya gabanin taron G20
“Idan Afirka ta haɗa kai bisa manufa ɗaya, za ta iya rinjayar ƙalubalen basussukanta tare da samar da ci-gaba ga jikokinmu na Afirka da za su zo nan gaba,” in ji Shugaba John Mahama.

11 May, 2025
Aljeriya ta kori jami’an leƙen asirin Faransa biyu daga ƙasarta kan kama su da fasfon bogi
Tashar talabijin ta Aljeriya ta ruwaito cewa mutanen biyu suna aiki ne ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta Faransa, a sashen Tsaron Cikin Gida, kuma sun “gaza bin ƙa’idojin doka” wajen shiga kasar Aljeriya.

11 May, 2025
Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 62 a Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo
Ruwan saman da aka rinƙa sheƙawa ya ƙara wa ambaliyar ƙarfi, inda ruwan ya shafe gidaje da kuma katse hanyoyin sadarwa.

11 May, 2025
Gwamnatin Nijar ta haramta fitar da dabbobi daga ƙasar gabanin Sallar Layya
Gwamnatin ta Nijar ta haramta fitar da shanu da raguna da awaki da raƙuma gabannin Babbar Sallah domin daƙile irin yadda farashinsu ke tashin gwauron zabi.

9 May, 2025
Yakin Sudan: Jiragen yaki marasa matuka sun yi luguden wuta a Port Sudan
Sabbin hare-haren sun sanya tsoron samun karancin man fetur da tabarbarewar rikicin jinkai.

8 May, 2025
Rikici a Sudan ta Kudu ya hana kai kayan agaji ga yara 60,000 da ke fama da tsananin yunwa
A tsakiyar watan Afrilu, an tilasta wasu jiragen ruwa dauke da tan 1,000 na abinci da kuma sauran kayan abinci masu gina jiki da suka nufi jihar Upper Nile koma wa saboda rashin tsaro, in ji WFP da UNICEF.

8 May, 2025
Mayaƙan RSF sun ƙaddamar da sabbin hare-hare a gabashi da kudancin Sudan
RSF ta kai sabbin hare-haren ne a babban sansanin sojin ruwa da ke wajen Port Sudan, da kuma wasu daga cikin defo-defo na fetur a kudancin birnin Kosti, kamar yadda wata majiyar soji da ta buƙaci a sakaya sunanta ta bayyana.

7 May, 2025
Tawagar IMF ta gana da Firaministan Nijar game da garambawul kan tattalin arzikin ƙasar
“Nijar za ta iya dogaro kan IMF saboda muna da dangantaka mai kyau, musamman ta ɓangaren samar da rance da kuma juriya na ɗorewa [na lamurra],” in ji jami’in na IMF.

6 May, 2025
Sudan ta yanke alaƙar diflomasiyya da ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa
Gwamnatin sojojin Sudan ta yanke alaƙar diflomasiyya da Lamuran ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, tana bayyana kasar a matsayin “mai yin katsalandan.”
