1 Aug, 2026

‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati

Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Jamhuriyar Nijar ANP bai faɗi adadin sojojin da aka kashe ba, sai dai ya tabbatar da cewa an kashe sojoji a harin da aka kai a kusa da garin N’Guigmi da ke yankin Tafkin Chadi.

f438e0ac 1754 4ec4 8b4a c8aca37ab490 1780422303460

31 Jul, 2026

Adadin ‘yan ci-ranin da suka rasu ya kai 19 bayan dubbai sun tsallaka zuwa yankin Ceuta na Sifaniya

Sifaniya ta tura dakaru tare da rufe kan iyakarta a Melilla bayan an samu isowar mutane da yawa daga Maroko, yayin da Rabat ke ƙoƙarin hana ƙarin tsallakewar mutane.

65b8fbcc 9bbd 4aee b91a 312aecf64676 1785443012641

31 Jul, 2026

Gwamnatin Ghana ta amince da shawara ƙara wa’adin mulkin shugaban ƙasa

Shawarar na daga wani ɓangare na shirin gyaran kundin tsarin mulkin Ghana.

9f62aeb8 6b9c 408d 9105 09d0403bfd08 1785489446555

30 Jul, 2026

Biranen Afirka 25 da Amurka za ta rufe ayyukan bayar da biza daga ranar 1 ga Agustan 2026

A tsakiyar watan Yulin 2026, Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta sanar da dakatar da bayar da biza daga birane 25 a faɗin Afirka, inda tilas masu neman bizar su tafi wasu biranen a abin da Washington ta bayyana “cibiyoyin yanki.”

dace2f0a 9871 4ceb 9e78 aeccb8f022db 1785350261057 main

28 Jul, 2026

Nijar ta dakatar da kamfanonin dillancin siminti 36 kan zargin ɓoye shi don haddasa ƙarancinsa

Gwamnatin ta Nijar ta zargi dillalan da boye siminti mai yawa duk da shirin gwamnati na sayar da siminti a farashi mai rangwame domin sauƙaƙa wa jama’a samun kayan gini.

640d8a9c 2373 44a8 a991 7253e9f9279c 1785227611025

28 Jul, 2026

Hukumomin Libya a Benghazi sun kori baƙin-haure fiye da 117,000 daga ƙasar

Akwai ‘yan Sudan fiye da 100,000 waɗanda suka amince su koma ƙasarsu bisa raɗin kansu yayin da hukumomin na Libya suka fitar da baƙin-haure 117,350 aƙalla daga ƙasar.

93ed29a2 74c0 4525 a5ce b34152b9003c 1785216324302

27 Jul, 2026

Mutumin da ya fi kowa tsawo a Ghana Awuche ya rasu

Sulemana Abdul Samed, wanda ake ganin shi ne namijin da ya fi kowa tsawo a Ghana, ya rasu yana da shekara 32, kamar yadda kafar watsa labaran ƙasar(GBC), ta ruwaito ranar Litinin.

9648c84c 845d 4d5e 8c58 be14e566a903 1785168815308 main

27 Jul, 2026

Chadi ta sanar da shirin janyewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC)

Daga cikin bincike 13 da kotun ta gudanar tun lokacin da ta fara aiki, tara sun shafi ƙasashen Afirka ne, yayin da huɗu kacal aka gudanar da su a sauran yankunan duniya “amma ba tare da samun wani ci-gaba na a-zo-a-gani ba,” a cewar gwamnatin Chadi.

f2992b34 365b 4048 b455 6b7ef77fa133 1778580041530 main

27 Jul, 2026

An gudanar da zanga-zanga a Tripoli saboda tsadar rayuwa da tabarbarewar ayyukan gwamnati

Masu zanga-zangar sun yi tir da matsalar wutar lantarki, yawan katsewar ruwa, raunin tsarin kiwon lafiya da kuma hauhawar farashin kayayyaki, a cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Libya.

73b34ef9 139f 4cb2 aafc 3a8b969f08d2 1785148914867

25 Jul, 2026

Ƙarin ma’aikatan jinya sun shiga yajin aiki yayin da cutar Ebola ta kama kusan mutum 3,000

Adadin waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar Ebola a Kongo ya kai 2,973, ciki har da mutum 1,309 da suka mutu, in ji ƙididdigar da gwamnati ta fitar ranar Jumma’a a batun da hukumomi suka tabbatar cewa shi ne yaɗuwar cutar da ta fi sauri a tarihi.

17f6e5ea 6a29 4b5f 85ae 26c29d47bcda 1784983975871
Ana lodawa...