18 Jun, 2026

An ji ƙarar harbe-harbe a kusa da babban filin jirgin sama na Nijar da ke Yamai

Kafofin watsa labaran cikin gida sun rawaito cewa an rufe hanyoyin shiga filin jirgin, sannan jami’an tsaro sun mayar da martani kan harin.

620d3fe5ea45503f663677ad31e1093223a447740aa14a720a97494546e282ec

16 Jun, 2026

An kama mutum da kunamu 150 ɓoye a tufafinsa a filin jirgin sama na Afirka ta Kudu

Jami’ai sun gano wanda ake zargin ne ta hanyar amfani da kwatancen da aka bai waɗanda ke wurin kafin su kama shi su kuma bincika jakunkunansa.

8b370682 4ee4 4ebd 811e d957ff80a8a6

15 Jun, 2026

Sojoji sun ce an kashe gomman mayaƙan RSF a hare-hare da aka kai a faɗin Sudan

Sojojin Sudan sun faɗa a ranar Lahadi cewa sun kashe gomman mayaƙan sa-kai na Rapid Support Forces (RSF) kuma sun hallaka motocin yaƙi 141 a hare-haren da suka kai a faɗin ƙasar a wannan watan.

2026 05 27t143749z 1 lynxmpem4q1m1 rtroptp 3 sudan politics survivors main

13 Jun, 2026

Uganda ta yi Allah wadai da takunkumin tafiye-tafiye ga ‘yan ƙasarta kan cutar Ebola

Ƙasar Uganda ta nuna rashin jin daɗinta dangane da yadda wasu ƙasashen duniya suka hana matafiya daga Uganda shiga ƙasashensu saboda fargabar cutar Ebola. Amurka, Canada da U.A.E na daga cikin ƙasashen da suka ɗauki wannan mataki.

2026 06 12t120226z 1 lynxmpem5b0ur rtroptp 3 health ebola congo 1

12 Jun, 2026

Nijar za ta karɓi tallafin dala miliyan 33 daga IMF

IMF ya ce tattalin arzikin Nijar ya ci gaba da kasancewa mai ƙarfi, inda ya bunƙasa da kashi 6.9 cikin 100 a shekarar 2025, kuma ana hasashen zai kai kashi 7 cikin 100 a shekarar 2026.

9e1960930b799570172af6ee63b79877c462e4cf30385b5e1887839c07868f2b

11 Jun, 2026

An cim ma yarjejeniyar zaman Lafiya tsakanin Manoma da makiyaya a Jihar Maradi ta Jamhuriyar Nijar

An cim ma yarjejeniyar ne a ranar 9 ga Yunin 2026 a yankin Sarkin Yamma inda wakilan manoma da makiyaya daga gundumomin Safo da Sarkin Yamma da kuma Tibiri da birnin Maradi suka sanya hannu kan yarjejeniyar.

2026 05 25t130423z 284721055 rc20dlab9hb2 rtrmadp 3 sudan politics food security

6 Jun, 2026

Mali ta ɗaure jami’in diflomasiyyar Faransa shekara 20 a gidan yari kan zargin neman haddasa rikici

Mali na zargin jami’in na ƙasar Faransa da aiki tare da Hukumar Leƙen Asiri ta Faransa domin neman hargitsa ƙasar.

2026 04 27t165442z 1471508492 rc2dwkaj6vez rtrmadp 3 mali security 1

5 Jun, 2026

An yi wa jagoran ‘yan adawa na Guinea Bissau ɗaurin talala

Wata kotun soji a ƙasar Guinea Bissau ta ba da umarni ranar Alhamis cewa a tsare jagoran ‘yan adawa Domingos Simoes Pereira a gida bayan an yi masa tambayoyi game zargin kitsa yi wa gwamnati juyin mulki.

ca86623796bf2e854e854fe4654e0b2f6ebb6c9219fc6d8c3dce3ed5b0ea9f90

5 Jun, 2026

Ƙishirwa ta kashe mutum 49 a saharar Nijar bayan motarsu ta lalace

Mamatan na cikin waɗanda ke dawowa daga ƙasar Mali domin bukukuwan Babbar Sallah a lokacin da motarsu ta lalace sannan ruwansu ya ƙare, kamar yadda ofishin gwamnan Jihar Agadez ya bayyana a wani saƙon da ta wallafa a shafin Facebook.

ad6f122b14762d6971d72b76adfad9ac9089a6bdc7207ae3f4f09724d6cc5dcd

4 Jun, 2026

Turkiyya da Nijar sun sanya hannu yarjejeniyoyin hadin kai bayan tattaunawar shugabannin kasashen

Kasashen Turkiyya da Niger sun rattaba hannu kan jerin yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a ranar Alhamis a gaban Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, da Shugaban Nijar, Abdourahamane Tiani.

83fc26155b29b4f366809039e9eeb0c2c6cb75940e37d907f3d8c798acd0b2c5 main
Ana lodawa...