Manyan jami’an AES na tattaunawa a Ouagadougou gabannin tattaunawar ƙungiyar da ECOWAS

Ana sa ran mahalarta taron za su mayar da hankali kan samar da wani daftari na musamman wanda zai zama jagora ga ƙungiyar AES wajen tattaunawa da ECOWAS kan muhimman batutuwan yankin.
25 Jun, 2026
Nijeriya da ƙasashe 4 sun ƙaddamar da sabuwar hukuma kan hanyar Abidjan zuwa Lagos ta $16bn

Aikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin yankin na faɗaɗa haɗin kai na tattalin arziki da kuma inganta haɗe abubuwa more rayuwa a fadin Yammacin Afirka
25 Jun, 2026
Nijar ta gabatar da takardar ficewa daga Kotun Kasa da Kasa ta Hukunta Manyan Laifuka, ICC

A cikin wata sanarwa da aka aiko wa AFP a ranar Talata, ICC ta ce ta karɓi “takardar ficewa” ranar 18 ga Yuni daga Nijar, da Janar Abdourahamane Tiani ke jagoranta.
24 Jun, 2026
Nijar ta gindaya wa Benin sharruɗa kan sake buɗe iyakar kasashen biyu

Rahotanni sun ce a ranar Lahadi ne wata babbar tawaga ta gabatar da waɗannan buƙatun yayin tattaunawar diflomasiyya.
22 Jun, 2026

MDD ta yi gargadi kan barazanar ‘babban zalunci kan bil’adama’ da ke tafe a birnin El-Obeid na Sudan

Cutar Ebola: Ma’aikatan lafiya 17 sun rasu yayin da cutar ke ‘yaɗuwa cikin sauri’

Aljeriya da Benin sun nuna goyon baya ga Nijar bayan hari kan filin jiragen sama

Ghana ta nemi a biya diyyar cinikin bayi

Harin da aka kai filin jirgin saman Nijar ya kashe jami’an tsaro 11, in ji gwamnati
18 Jun, 2026
An ji ƙarar harbe-harbe a kusa da babban filin jirgin sama na Nijar da ke Yamai
Kafofin watsa labaran cikin gida sun rawaito cewa an rufe hanyoyin shiga filin jirgin, sannan jami’an tsaro sun mayar da martani kan harin.

16 Jun, 2026
An kama mutum da kunamu 150 ɓoye a tufafinsa a filin jirgin sama na Afirka ta Kudu
Jami’ai sun gano wanda ake zargin ne ta hanyar amfani da kwatancen da aka bai waɗanda ke wurin kafin su kama shi su kuma bincika jakunkunansa.

15 Jun, 2026
Sojoji sun ce an kashe gomman mayaƙan RSF a hare-hare da aka kai a faɗin Sudan
Sojojin Sudan sun faɗa a ranar Lahadi cewa sun kashe gomman mayaƙan sa-kai na Rapid Support Forces (RSF) kuma sun hallaka motocin yaƙi 141 a hare-haren da suka kai a faɗin ƙasar a wannan watan.

13 Jun, 2026
Uganda ta yi Allah wadai da takunkumin tafiye-tafiye ga ‘yan ƙasarta kan cutar Ebola
Ƙasar Uganda ta nuna rashin jin daɗinta dangane da yadda wasu ƙasashen duniya suka hana matafiya daga Uganda shiga ƙasashensu saboda fargabar cutar Ebola. Amurka, Canada da U.A.E na daga cikin ƙasashen da suka ɗauki wannan mataki.

12 Jun, 2026
Nijar za ta karɓi tallafin dala miliyan 33 daga IMF
IMF ya ce tattalin arzikin Nijar ya ci gaba da kasancewa mai ƙarfi, inda ya bunƙasa da kashi 6.9 cikin 100 a shekarar 2025, kuma ana hasashen zai kai kashi 7 cikin 100 a shekarar 2026.

11 Jun, 2026
An cim ma yarjejeniyar zaman Lafiya tsakanin Manoma da makiyaya a Jihar Maradi ta Jamhuriyar Nijar
An cim ma yarjejeniyar ne a ranar 9 ga Yunin 2026 a yankin Sarkin Yamma inda wakilan manoma da makiyaya daga gundumomin Safo da Sarkin Yamma da kuma Tibiri da birnin Maradi suka sanya hannu kan yarjejeniyar.

6 Jun, 2026
Mali ta ɗaure jami’in diflomasiyyar Faransa shekara 20 a gidan yari kan zargin neman haddasa rikici
Mali na zargin jami’in na ƙasar Faransa da aiki tare da Hukumar Leƙen Asiri ta Faransa domin neman hargitsa ƙasar.

5 Jun, 2026
An yi wa jagoran ‘yan adawa na Guinea Bissau ɗaurin talala
Wata kotun soji a ƙasar Guinea Bissau ta ba da umarni ranar Alhamis cewa a tsare jagoran ‘yan adawa Domingos Simoes Pereira a gida bayan an yi masa tambayoyi game zargin kitsa yi wa gwamnati juyin mulki.

5 Jun, 2026
Ƙishirwa ta kashe mutum 49 a saharar Nijar bayan motarsu ta lalace
Mamatan na cikin waɗanda ke dawowa daga ƙasar Mali domin bukukuwan Babbar Sallah a lokacin da motarsu ta lalace sannan ruwansu ya ƙare, kamar yadda ofishin gwamnan Jihar Agadez ya bayyana a wani saƙon da ta wallafa a shafin Facebook.

4 Jun, 2026
Turkiyya da Nijar sun sanya hannu yarjejeniyoyin hadin kai bayan tattaunawar shugabannin kasashen
Kasashen Turkiyya da Niger sun rattaba hannu kan jerin yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a ranar Alhamis a gaban Shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdoğan, da Shugaban Nijar, Abdourahamane Tiani.



