Shugaban sadarwa na Turkiyya ya ce Isra’ila na yi wa yunƙurin zaman lafiya na Gaza zagon ƙasa

Burhanettin Duran ya bayyana ƙudirin Turkiyya na jajircewa wajen tabbatar da halastattun haƙƙoƙin Falasɗinawa.
3 Aug, 2026
Turkiyya ta kama ɗanta’addan FETO da ake nema bisa ƙoƙarin kashe Shugaba Erdogan a shekarar 2016

Wanda ake zargin, wani keftin na soji da aka kora kuma tsohon matuƙin helikwafta, ya kasance ana nemansa ruwa-a-jallo a ƙarƙashin wata Jar Sanarwar ta Hukumar ‘Yansandan Duniya.
1 Aug, 2026
Turkiyya ta yi fice a Gasar Duniya ta Rubutu a Kwamfuta da kambi 36

Masu gogayya daga kasashe 34 sun gwada saurin rubutu da rashin kuskure a wajen Gasar Rubutu a Kwamfuta ta Duniya ta Intersteno da ke gudana a Liverpool.
31 Jul, 2026
Turkiyya da Nijeriya sun ƙara ƙarfafa daɗin gwiwa kan ƙera jiragen ruwa

Gwamnatin Nijeriya na son kamfanonin ƙera jiragen ruwa na Turkiyya su zama abokan hulɗa na dindindin wajen haɓaka ƙarfin ƙasar na ƙera jiragen ruwa a cikin gida.
29 Jul, 2026

Turkiyya ta yi kira ga Amurka da Iran su koma kan yarjejeniya, su kuma yi aiki tare da Qatar

Girgizar ƙasa mai maki 5 ta girgiza gabashin Turkiyya

Daƙile yunƙurin juyin mulki na 2016 ya ‘bayyana ‘yancin kai’ na ƙarni ga Turkiyya, in ji Erdogan

Turkiyya na juyayin cika shekaru 10 da yunƙurin juyin mulki na ranar 15 ga Yuli da bai yi nasara ba

Jami’an leƙen asiri na Turkiyya sun kama wani babban jami’in Daesh a Syria
11 Jul, 2026
Manufofi da gwamnatin Netanyahu ‘nauyi’ ne ga Isra’ila da yankin da tsaron duniya: Ministan Turkiyya
Ministan harkokin wajen Turkiyya Hakan Fidan ya ce ‘Turkiyya na da matsaya ta musamman ta iya shiga tsakani kan rigingimun yanki, domin ‘mun san kowa, mun san yanayin ko wane rikici’.

9 Jul, 2026
Shugaba Erdogan ya ce taron NATO a Ankara ‘nasara ce ta tarihi’
Shugaban ƙasar Turkiyya Recep Erdogan ya ce babban taron NATO ya ƙarfafa haɗin kan ƙawayen inda ya kuma ce Trump ya ɗauki mataki mai kyau game da Turkiyya kan shirin F-35.

7 Jul, 2026
Taron Trump-Erdogan: Amurka za ta ɗage wa Turkiyya takunkumai, za a yanke hukunci kan f-35 nan kusa
Shugaban Amurka ya ce Washington ba ta son saka wa ƙawayenta takunkumi yayin da shi da Shugaba Erdogan suka sha alwashin ƙarfafa haɗakar tsaro da faɗaɗa alaƙa gabanin Taron Koli na shugabannin NATO a Ankara.

7 Jul, 2026
Tsaron Turai ba zai ta’allaka ga Tarayyar Turai ba, in ji Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan
Fidan ya ce Turkiyya na da babbar rawar takawa a tsaron Turai inda ya yi kira a faɗaɗa ƙawancen tsaro a NATO sama da Tarayyar Turai kaɗai.

6 Jul, 2026
Turai za ta yi amfani da taron NATO a Ankara ta nuna wa Trump kyakkyawar niyyarta kan tsaro: Jamus
Jamus tana haɗa kan ƙasashen Turai a ƙawancen NATO da kuma ƙawaye a Tarayyar Turai don ƙarfafa ikon soji da faɗaɗa haɗin kai na masa’antar tsaro da kuma gaggauta ƙera manyan makamai, a cewar mataimakin ministan tsaro Nils Schmid.

4 Jul, 2026
Shugaban Turkiyya Erdogan ya karɓi baƙuncin Firaministan Pakistan Sharif a Istanbul
Bayan bikin tarbar firaministan wanda aka yi a hukumance, shugabannin biyu sun tafi ƙai tsaye domin tattaunawa a kan abubuwan da suka shafi ƙasashensu.

30 Jun, 2026
Tawagar majalisar dokokin NATO ta ziyarci kamfanin Baykar mai ƙera jirage marasa matuƙa a Ankara
An yi wa tawagar bayani game da fasahar tsaro ta Baykar da kuma ayyuka na ƙirƙire-ƙirƙire gabannin taron NATO da za a yi a Ankara tsakanin ranar 7 zuwa 8 ta watan Juli.

29 Jun, 2026
Mataimakin Shugaban Kasar Turkiyya na neman a bunkasa kasuwanci a tsakanin duniyar Musulunci
Cevdet Yilmaz ya bayyana habakar tattalin arzikin Turkiyya da mambobn OIC, yana mai cewa kasuwanci a tsakaninsu ya kai dala biliyan 118 a shekarar bara, inda tattalin arzikin kasar ya haura dala tiriliyan 1.6.

28 Jun, 2026
Ma’aikatan agajin Turkiyya sun fara aikin ceto a Venezuela bayan girgizar ƙasa
Ma’aikata daga Hukumar Kula da Ayyukan Gaggawa da Kiyaye Afkuwar Bala’o’i ta Turkiyya (AFAD) da Rundunar Sojin Turkiyya sun isa La Guaira, ɗaya daga cikin wuraren da girgizar ƙasa ta fi yi wa illa.

26 Jun, 2026
Turkiyya ta tura tawagar bincike da ceto zuwa Venezuela bayan iftila’in tagwayen girgizar kasa
A yau Juma’a wasu jiragen saman sojin biyu, dauke da ma’aikatan bincike da ceto, da kungiyoyin likitoci da kayan agaji, za su tashi daga Istanbul zuwa Venezuela.



