Nijeriya

NDLEA Ta Kama Sama da Mutane 77,000, Ta Ƙwace Miyagun Ƙwayoyi Fiye da Kilo 14,000 a Shekara Biyar

NDLEA ta ce cikin shekaru biyar ta kama kusan mutane 78,000 tare da ƙwace fiye da kilo 14,000 na miyagun ƙwayoyi, tana jaddada cewa Nijeriya ba za ta zama cibiyar fataucin ƙwayoyi ba.

Newstimehub

Newstimehub

20 Jan, 2026

a545d73e41305f249895b3b7b2bf7ff53cbb8e1e42eb4c874cdd82b2b7920587

A wani rahoto da ke nuna irin tsananin yaƙin da Nijeriya ke yi da safarar miyagun ƙwayoyi, Hukumar NDLEA ta bayyana gagarumar nasara da ta samu cikin shekaru biyar, inda ta katse hanyoyin masu fataucin ƙwayoyi tare da kama dubban mutane da ƙwace tarin miyagun abubuwa, abin da ya kara nuna cewa ƙasar ba za ta zama mafakar laifi ba.

Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa, ya ce daga cikin shekaru biyar da suka wuce, hukumar ta kama mutum 77,792 tare da ƙwace kilo 14,847 na miyagun ƙwayoyi. Ya ce an kuma kama manyan jagororin fataucin ƙwayoyi 128, yayin da kotuna suka yanke wa mutane 14,225 hukuncin dauri.

A bangaren gyaran hali, sama da masu shan ƙwayoyi 32,000 sun amfana da shirin warkarwa, yayin da aka gudanar da dubban shirye-shiryen wayar da kai a faɗin ƙasar. Marwa ya danganta nasarorin da ingantaccen tattara bayanan sirri, haɗin gwiwa da hukumomi, da kuma sake fasalin NDLEA domin ƙara inganci.

Majiyar Labari: TRT HAUSA