Gwamnatin Iran ta bayyana cewa za ta ɗauki kowane irin hari daga Amurka a matsayin cikakken yaƙi a kanta, yayin da rahotanni ke nuna cewa manyan jiragen yaƙin Amurka, ciki har da jirgin ɗaukar jiragen sama, na dab da isa yankin Gabas ta Tsakiya.
Wani babban jami’in tsaro na Iran ya ce an sanya dakarun ƙasar cikin shirin ko-ta-kwana, yana mai jaddada cewa Tehran ba za ta bambance ko hari ƙarami ne ko babba ba – duk za a ɗauke shi a matsayin yaƙi kai tsaye.
“Ba ma fatan a kai ga faɗa, amma sojojinmu sun shirya kan duk wani abu mafi muni,” in ji jami’in.
“Idan aka kai mana hari, za mu mayar da martani da dukkan ƙarfin da muke da shi.”
Shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar da cewa jirgin ɗaukar jiragen yaƙi na USS Abraham Lincoln da wasu rundunonin soji suna kan hanyarsu zuwa yankin, amma ya ce yana fatan ba za a yi amfani da su ba.
Jami’in Iran ya kuma ce ƙasar ba za ta yarda a take mata ‘yanci ko ikon yankinta ba, kuma duk wata barazana za ta fuskanci martani mai tsauri.














