Gabas Ta Tsakiya Tsaro

Drones Biyu Sun Fadi Kusa da Filin Jirgin Sama na Dubai, Mutane Hudu Sun Jikkata

Faduwar drones biyu kusa da filin jirgin sama na Dubai ta jikkata mutane hudu, yayin da tashin hankali ke ci gaba da karuwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

Newstimehub

Newstimehub

11 Mar, 2026

JJ 1

Wasu jirage marasa matuki guda biyu sun fadi a ranar Laraba kusa da filin jirgin sama na Dubai International Airport, lamarin da ya jikkata mutane hudu, kamar yadda ofishin yada labarai na Dubai ya bayyana.

Rahoton ya ce wadanda suka jikkata sun hada da ‘yan kasar Ghana biyu da dan kasar Bangladesh guda daya da suka samu raunika kadan. Haka kuma wani dan kasar India ya samu raunuka masu tsanani kadan amma yana samun kulawar likitoci.

Duk da faruwar lamarin, hukumomin Dubai sun tabbatar da cewa zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin na Dubai International Airport na ci gaba da tafiya kamar yadda aka saba, ba tare da wani cikas ba.

Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke kara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya bayan harin hadin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, wanda ya jawo mutuwar mutane sama da 1,200. Bayan haka Tehran ta mayar da martani ta hanyar kai hare-haren drones da makamai masu linzami kan wasu wurare a Isra’ila, Jordan, Iraq da kuma wasu kasashen Gulf da ke dauke da sansanonin sojin Amurka.

Majiyar Labari: AA