Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Pakistan ta soki sabuwar dokar Isra’ila da ta amince da hukuncin kisa ga fursunonin Falasɗinawa, tana mai cewa dokar ba ta dace da ka’idojin kasa da kasa ba kuma tana da matukar tsauri. Shugaban kungiyar, Asad Iqbal Butt, ya bayyana cewa wannan mataki na iya sa wasu ƙasashe su bi irin wannan hanya, wanda zai kara rikita tsarin doka a duniya.
Ya kuma jaddada cewa dokar ta sabawa dokokin kasa da kasa da kuma Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya. A cewarsa, idan kasashe suka fara aiwatar da irin wannan hukunci ga ‘yan kasashen waje, hakan na iya haifar da rikice-rikicen diflomasiyya masu tsanani har ma da yiwuwar barkewar sabbin rikice-rikice.
Majalisar dokokin Isra’ila (Knesset) ta amince da dokar da rinjayen kuri’u 62 kan 48, tare da goyon bayan Firayim Minista Benjamin Netanyahu. Dokar ta tanadi cewa za a aiwatar da hukuncin kisa ta hanyar rataya, inda jami’an gidan yari za su gudanar da shi cikin yanayin boye sunayensu tare da kariyar doka.
Majiyar Labari: AA














