Gwamnatin Amurka ta bukaci Isra’ila da ta guji kai sabbin hare-hare kan cibiyoyin makamashin Iran, musamman wuraren samar da man fetur. Rahoton kamfanin dillancin labarai na Axios ya ce an isar da wannan sako ga manyan jami’an Isra’ila har ma da babban hafsan sojin ƙasar, Eyal Zamir.
Washington ta bayyana cewa hare-hare kan cibiyoyin makamashi na iya shafar talakawan Iran kai tsaye, alhali da dama daga cikinsu suna adawa da gwamnatin Tehran. A cewar Amurka, irin wadannan hare-hare na iya kara tsananta halin da fararen hula ke ciki ba tare da warware rikicin ba.
Rahotanni sun ce tsohon shugaban Amurka Donald Trump na fatan cewa bayan rikicin ya lafa, za a iya yin hadin gwiwa da bangaren man fetur na Iran. Haka kuma yana damuwa cewa lalata cibiyoyin makamashi na Iran na iya jawo mayar da martani mai tsanani daga Tehran kan tashoshin mai a kasashen Tekun Fasha.
Wata majiya ta shaida wa Axios cewa Trump na kallon kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran a matsayin “zabi mai matukar hatsari”, wanda za a iya amfani da shi ne kawai idan Iran ta fara kai hari kan wuraren mai a kasashen Gulf. Wannan bukata ta Amurka ta zo ne bayan rahotannin da ke nuna Washington ba ta gamsu da yawan hare-haren da Isra’ila ta kai kan tankokin mai na Iran a karshen makon da ya gabata ba.














