Kungiyoyin ceto sun gano gawawwakin dukkan ma’aikatan ma’adanai guda biyar da suka makale a karkashin kasa bayan wani mummunan kwararar laka a ma’adinan Ekapa Minerals da ke Kimberley. Lamarin ya faru ne tun ranar 17 ga Fabrairu lokacin da laka mai dauke da ruwa da tarkace ta mamaye sassan ma’adinan ba tare da gargadi ba.
Ayyukan ceto sun dauki makonni, inda aka fara gano gawar farko a makon da ya gabata, sannan aka gano sauran a jere har zuwa ranar Litinin da aka kammala aikin. Rahotanni sun nuna cewa an kwashe fiye da mita kubik 32,000 na laka da ruwa domin isa ga wadanda suka makale.
Hukumar ‘yan sanda ta Afirka ta Kudu (SAPS) ta fara bincike kan lamarin domin gano musabbabin hatsarin. A lokaci guda, kamfanin da ke gudanar da ma’adinan ya nemi a rufe shi, yayin da aka dakatar da duk ayyukan hakar ma’adanai a wurin har sai an kammala bincike.
Wannan hatsari ya kara nuna matsalolin da ke addabar harkar ma’adanai a kasar, inda tsofaffin kayayyaki, hakar ba bisa ka’ida ba da kuma rashin kwanciyar kasa ke haddasa hadurra masu tsanani akai-akai.














