Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin tsare wasu mutum tara da ake zargi da laifin ta’addanci, bisa zargin kai harin kisan kiyashi a ƙauyen Yelwata na Benue a ranar 13 ga Yuni, 2025, wanda ya yi sanadin mutuwar kimanin mutane 150. Harin na daga cikin mafi muni da aka kai wa yankunan karkara a ‘yan shekarun nan.
Tuhume-tuhumen sun nuna cewa waɗanda ake ƙara sun shirya tarurruka, sun tara kuɗaɗe, sun sayi makamai, sannan suka haɗa ‘yan bindiga daga jihohi da dama kafin kai harin. Kotun ta ce ana zargin shugaban ƙungiyar, Ardo Lawal Mohammed Dono, da jagorantar shirye-shiryen daga Nasarawa, ciki har da bayar da umarni da ɗaukar mayaka.
Haka kuma, ana zargin wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma da samar da bindigogin AK-47, taimaka wa maharan da dabaru, ko ba su mafaka domin shiryawa da aiwatar da hare-hare. Masu gabatar da ƙara sun ce harin ya lalata gidaje da dama tare da janyo asarar rayuka masu yawa a gundumar Guma.
Benue, da ke Arewa ta Tsakiyar Nijeriya, ta shafe shekaru tana fama da rikice-rikicen manoma da makiyaya da na kabilanci. A matakin ƙasa da ƙasa, matsin lamba kan tsaron Nijeriya ya ƙaru bayan kalaman Donald Trump, yayin da hukumomin Nijeriya ke cewa suna ƙarfafa haɗin gwiwa da Washington domin inganta tsaro.














