Hukumar kula da filayen jiragen sama ta Najeriya, Federal Airports Authority of Nigeria, ta sanar da kama wasu mutane huɗu da ake zargi da fashin daji a filin jirgin saman Akure Airport da ke birnin Akure.
A cikin wata sanarwa da daraktan hulɗa da jama’a na hukumar, Henry Agbebire, ya fitar, an ce kamen ya biyo bayan rahoton da aka samu cewa wasu mutane da ba a amince da su ba suna zagaye a bayan katangar filin jirgin. Nan take jami’an tsaron filin jirgin tare da Nigeria Police Force da sauran jami’an tsaro suka ƙaddamar da wani aikin haɗin gwiwa domin bincike.
A yayin aikin, an ga wasu mutane suna ƙoƙarin tserewa daga wurin, amma jami’an tsaro sun samu nasarar kama huɗu daga cikinsu tare da miƙa su ga ‘yansanda domin ƙarin bincike. Hukumar FAAN ta yaba da haɗin gwiwar jami’an tsaro daban-daban da suka taimaka wajen wannan kamen.
Hukumar ta ce wannan lamari ya sake nuna muhimmancin ƙarfafa tsaro a filayen jiragen sama, inda gwamnatin tarayya ta fara aikin gina katangu na zamani a filayen jiragen sama a faɗin Nigeria domin inganta kariya da tsaron matafiya da dukiyoyin filayen jiragen sama.














