Akalla mutane shida sun rasa rayukansu bayan hare-haren da sojojin Amurka da Isra’ila suka kai kan yankunan zama a birnin Tabriz, cikin lardin East Azerbaijan na Iran, a daren Lahadi zuwa Litinin.
Rahotanni daga kamfanin dillancin labarai na Fars sun nuna cewa mutane hudu daga cikin wadanda suka mutu fararen hula ne, yayin da wasu shida suka jikkata sakamakon harin da aka kai kan wani gini a unguwar Nasr. Lamarin ya haifar da barna mai yawa a yankin.
A wani hari daban a yankin Rab-i Rashidi da ke arewa maso gabashin Tabriz, wasu karin mutane biyu sun rasa rayukansu, wanda ya kara yawan wadanda suka mutu zuwa shida gaba daya.














