Afirka

Chadi ta zama ƙasa mafi fama da gurɓataccen iska a Afirka

Rahoton IQAir ya nuna cewa Chadi ta fi fama da gurɓataccen iska a Afirka, yayin da yawancin ƙasashe duniya ke gaza cika ƙa’idar WHO.

Newstimehub

Newstimehub

24 Mar, 2026

b8a7dd1732799fce36ec6365192a4ace8d97953b512cc3c2060d5382f9813fdb

Wani bincike na kamfanin IQAir ya nuna cewa an sanya Chadi a matsayin ƙasa mafi fama da kura da gurɓataccen iska a Afirka a shekarar 2025, inda matakan ƙananan barbashi masu hatsari (PM2.5) suka wuce ƙa’idar da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta gindaya.

Rahoton ya kuma bayyana cewa yawancin ƙasashe a duniya ba su cika wannan ƙa’ida ba, inda ƙasashe 130 cikin 143 da aka bincika suka gaza.

A duniya baki ɗaya, Pakistan, Bangladesh da Tajikistan su ne ƙasashen da suka fi fama da gurɓacewar iska, yayin da yankin Bodele a arewacin Chadi ke daga cikin wuraren da ke samar da kura mafi yawa a duniya.

Masana sun nuna cewa rashin cikakken bayanai bayan rufe wasu shirye-shiryen sa ido na Amurka ya sa a wasu lokuta ba a iya tantance ainihin matakan gurɓatawar yadda ya kamata ba.

Rahoton ya kuma nuna cewa birnin Loni a India shi ne mafi gurɓacewa a duniya, sai Hotan a China, yayin da mafi yawan biranen da suka fi gurɓatawa suna cikin India, Pakistan da China. Haka kuma, kashi 14% ne kawai na biranen duniya suka cika ƙa’idar WHO a 2025, ƙasa da kashi 17% na shekarar da ta gabata, sakamakon abubuwa kamar gobarar daji da suka ƙara gurɓata iska a wasu yankuna.

Sai dai a gefe guda, wasu ƙasashe kamar Australia, Iceland da Estonia sun samu ingantuwar yanayin iska, yayin da ƙasashe 75 suka rage matakan PM2.5 idan aka kwatanta da 2024. Duk da haka, ƙasashe 54 sun fuskanci ƙaruwa a gurɓatawar iska, lamarin da ke nuna cewa matsalar har yanzu na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar al’umma.

Majiyar Labari: TRT HAUSA