Gwamnatin Italiya ta sake tabbatar da kudurinta na tallafawa shirin zaman lafiya da kuma sake gina Gaza Strip, kamar yadda Ministan Harkokin Wajen ƙasar, Antonio Tajani, ya bayyana. Ya ce Rome za ta ci gaba da taka rawar gani, tare da haɗa kamfanoni masu zaman kansu na Italiya a cikin ayyukan farfaɗo da yankin.
Tajani ya halarci wata ganawa da abokan hulɗar Turai da na yankin a gefen taron tsaro na Munich, inda batun sake gina Gaza ya kasance a sahun gaba. A cewarsa, Italiya na jagorantar wani shiri na dala miliyan 60 da ya haɗa da agajin jin ƙai, kawar da nakiyoyi, ƙarfafa bangaren lafiya da ilimi, da gyaran gidaje ga waɗanda rikici ya raba da muhallansu.
Ministan ya jaddada cewa fifiko na gaggawa shi ne dorewar tsagaita wuta, yana mai cewa babban buri shi ne samar da yanayin da zai ba da damar mafita ta ƙasashe biyu. Ya kuma yi gargadin cewa duk wani yunƙuri na mamaye ko haɗe yankunan Falasɗinu abu ne da ba za a amince da shi ba.
A halin da ake ciki, hukumomin Falasɗinu sun ce rikicin ya jawo asarar rayuka masu yawa tare da mummunar barna a Gaza, lamarin da ke ƙara nuna muhimmancin sake gina yankin da kuma nemo mafita ta siyasa mai ɗorewa.
Majiyar Labari: AA














