Mutane 14 sun jikkata a ranar Laraba bayan harba makamai masu linzami zuwa Isra’ila, a cewar hukumar agajin gaggawa ta Magen David Adom. Daga cikin waɗanda suka jikkata, akwai wata mata mai shekaru 36 da wani yaro mai shekaru 13 da suka samu raunuka masu tsanani zuwa matsakaici, yayin da sauran 11 suka samu ƙananan raunuka.
Hukumar ta bayyana cewa an garzaya da dukkan waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci domin samun kulawa. Wannan lamari na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin yankin Gabas ta Tsakiya ke ƙara tsananta tun bayan harin da Isra’ila da Amurka suka fara a ranar 28 ga Fabrairu kan Iran.
Iran ta mayar da martani da hare-haren jiragen sama marasa matuki da makamai masu linzami zuwa Isra’ila da wasu ƙasashe na yankin, lamarin da ya jawo asarar rayuka da barna ga dukiyoyi, tare da rikita harkokin kasuwanci da zirga-zirgar jiragen sama a duniya. Haka kuma, Isra’ila ta ƙara kai hare-hare a Lebanon tare da fara farmakin ƙasa bayan rikicin da Hezbollah.
Majiyar Labari: AA














