Rashin sa ido kan shigar da mai Nijeriya na barazana ga ayyukan yi da zuba jari: Dangote

Dangote ya bukaci a gudanar da bincike na hukuma a kan Hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Nijeriya, NMDPRA.
15 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta karyata zargin bai wa Faransa bayanan ‘yankasar don tara haraji

Sanarwar fadar Shugaban Nijeriya ta ce yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin Hukumar Tara Harajin Kasar, FIRS da wani kamfanin Faransa damar ganin bayanan masu biyan harajin Nijeriya ko manhajar int.
15 Dec, 2025
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP, sun lalata motocin ƙunar-baƙin-wake na ‘yan ta’adda

‘Yan ta’addan sun yi yunkurin kutsawa cikin sansanin soji na Mairari ta hanyar amfani da motocin ƙunar-baƙin-wake guda biyu. Sai dai sojojin da ke aikin sa ido sun gano tare da tarwatsa motocin kafin su kai ga shiga sansanin.
14 Dec, 2025
Shugaba Tinubu ya amince da kafa sabuwar makarantar horar da kuratan sojoji a Abakaliki

Shugaban Sojin Ƙasa na Nijeriya Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya ce ana sa ran sabon depot ɗin da za a buɗe a Abakaliki zai fara aiki nan gaba kaɗan sannan kuma ya tallafa wa sauran wuraren horar da kuratan soji da ke Zaria da Osogbo.
13 Dec, 2025

Kotun Ƙolin Nijeriya ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda ta tabbatar da hukuncin kisa

Aƙalla sojojin Nijeriya da Ivory Coast 200 sun isa Benin bayan an daƙile yunƙurin juyin mulki

Majalisar Wakilan Nijeriya ta nemi gwamnati ta bayar da rangwamen haraji ga kamfanonin jiragen sama

Saɓanin da ya kunno kai tsakanin Majalisar Dattijan Nijeriya da Shugaba Tinubu kan janye ‘yansanda

Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kashe ɓarayin daji 11 a Sokoto
11 Dec, 2025
Remi Tinubu ta yi watsi da zargin tsayar da gwamnan Osun daga yin waka a taron nadin sarautarta
A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Talata, Remi Tinubu ta ce, ‘‘Masu suka sukan mayar da ƙaramin abu ya zama babba, kuma hakan na haifar da ruɗani a yanayin shugabanci.’’

9 Dec, 2025
Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tura sojoji Jamhuriyar Benin
Bayan shugaba Bola Tinubu ya miƙa buƙatar neman amincewar majalisar, a zamanta na ranar Talata Majalisar Dattijan Nijeriya ta amince da tura sojojin wanzar da zaman lafiya zuwa Jamhuriyar Benin.

9 Dec, 2025
Rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta keta sararin samaniyar Burkina Faso
Rundunar sojin saman Nijeriya ta ce jami’anta suna cikin aminci kuma sun sami tarba mai kyau a Burkina Faso, sai dai kuma ƙungiyar AES ta ce duk wani jirgin da ya keta alfarmar sararin samaniyarta za a yi kaca-kaca da shi.

9 Dec, 2025
An Saki Wasu Dalibai a Nijeriya, Amma Daruruwan Yara Har Yanzu Na Hannun ‘Yan Bindiga
Bayan sama da makonni biyu a cikin daji, an fara sakin wasu yara, yayin da daruruwan suke ci gaba da fuskantar barazanar rayuwa.

9 Dec, 2025
Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi ɗalibai 100 na St. Mary’s Catholic School da aka ceto
Ɗaliban na makarantar St. Mary’s Catholic School sun isa gidan gwamnatin Jihar Neja ne a cikin motocin bas da misalin ƙarfe 5:20 na yamma sannan Gwamna Bago da wasu jami’an gwamnatinsa suka tarbe su.

8 Dec, 2025
Kotu ta yi watsi da buƙatar Nnamdi Kanu ta a ɗauke shi daga gidan gyaran yari na Sokoto
Mai shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya ƙi amincewa da buƙatar Nnamdi Kanu, jagoran ƙungiyar IPOB, ta a ɗauke shi daga gidan gyaran hali na Sokoto uzwa Abuja ko kuma Jihar Nasarawa mai maƙwabtaka.

8 Dec, 2025
Shugaba Tinubu ya jinjina wa sojojin Nijeriya kan daƙile juyin mulki a Benin
Bayan buƙatar da gwamnatin Benin ta yi sau biyu, Shugaba Bola Tinubu ya umarci jiragen yaƙin Nijeriya su shiga ƙasar inda suka ƙwace ikon sararin samaniyarta domin daƙile masu iƙirarin juyin mulkin da ke gidan talbijin na ƙasar da wani sansanin soji.

8 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta karɓo ɗalibai 100 da aka sace daga St. Mary’s Catholic School a Jihar Neja
‘Yanbindiga sun kai hari a makarantar St. Mary’s Catholic School da ke Papiri a Jihar Neja ne ranar 21 ga watan Nuwamba inda suka sace mutum 315 — ɗalibai 303 da malamai 12.

7 Dec, 2025
Tawagar Majalisar Dokokin Amurka ta isa Nijeriya, ta tattauna da Nuhu Ribadu
Babban Mai Bai wa Shugaban Nijeriya Shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu ya ce tawagar ta je Nijeriya ne domin tattara bayanai bayan tattaunawar diflomasiyya da tawagar Nijeriya ta yi a Washington a kwanakin baya kan zargin tauye haƙƙin addini.

6 Dec, 2025
Gwamnatin Nijeriya za ta fara rufe wuraren sana’ar POS marasa rajista daga Janairun 2026
Hukumar da ke yi wa Kamfanonin Rajista a Nijeriya ta yi gargaɗi game da masu gudanar da sana’ar POS ba tare da rajista ba inda ta ce daga Janairun 2026, jami’an tsaro za su fara rufe duk wani wurin sana’ar POS maras rajista.



