Gwamnatin Jihar Katsina za ta shirya muƙabala tsakanin Yahya Masussuka da sauran Malaman Musulunci

“Domin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, gwamnan Jihar Katsina Umaru Dikko Radda ya umarci Malam Yahya ya shirya kare kansa bisa zargin da ake masa a gaban majalisar malamai,” in ji sanarwar.
18 Nov, 2025
Babban hafsan sojin Nijeriya ya je Jihar Kebbi ya nemi a tsaurara neman ‘yan matan da aka sace

Janar Shaibu ya bayar da umarnin ne a ranar Litinin, 17 ga Nuwamban 2025, yayin wata ziyarar aiki da ya kai jihar.
18 Nov, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta umarci jami’an tsaro su kuɓutar da ɗalibai mata da aka sace a Jihar Kebbi

“An umarci jami’an tsaronmu da jami’an leƙen asiri su gano, tare da kuɓutar da ɗaliban da kuma dawo da su cikin aminci,” a cewar Minitstan Watsa Labarai na Kasar, Mohammed Idris a cikin wata sanarwa.
18 Nov, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da tallafin jarin N50m ga ɗalibai a fannin ƙirƙire-ƙirƙire

Shirin zai taimaka wajen gano da horar da matasa manyan gobe ‘yan Nijeriya tare da samar da hanyar tallafawa ƙirƙire-ƙirƙirensu masu mahimmaci a fannonin Kimiyya da Fasaha da Injiniyanci da Lissafi da kuma Kimiyyar Lafiya wato (STEMM).
17 Nov, 2025

Nijeriya tana tattaunawa kan tsaro da Amurka bayan barazanar Trump: Yusuf Tuggar

‘Yan sandan Nijeriya sun tabbatar da sace ɗalibai ‘yan mata 25 a Kebbi

Sojojin Nijeriya sun daƙile kwanton-ɓauna, sun yi watsi da jita-jitar sace wani janar na soja

Kasafin kuɗin gwamnatin kano na 2026 zai haura naira tiriliyan ɗaya – Gwamna Abba Kabir

Rundunar sojin Nijeriya ta ƙuɓutar da ‘yan bautar ƙasa 47 daga ‘yan Boko Haram a Borno
13 Nov, 2025
Ministan Abuja Nyesom Wike ya ce yana girmama sojoji
Ya ce gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙuri na karya ƙa’idojin amfani da filaye ko kuma hana jami’an gwamnati gudanar da ayyukansu da ke kan ka’ida ba.

13 Nov, 2025
Nijeriya ta dakatar da aiwatar da harajin kashi 15% kan shigar da fetur da dizal cikin ƙasar
Tun farko manufar wannan matakin ita ce ƙarfafa masana’antun tace man cikin gida kamar su Matatar Dangote da ƙananan masana’antun tace mai, ta hanyar sanya man da ake shigar da shi daga waje ya fi tsada.

13 Nov, 2025
‘Musulmai ne Boko Haram ta fara yi wa ɓarna’: AU ta yi watsi da Trump kan kisan kiyashi a Nijeriya
A farkon wannan watan Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirye-shiryen yiwuwar kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.

12 Nov, 2025
Za mu bai wa kowane jami’in soja da ke bakin aikinsa kariya – Ministan Tsaron Nijeriya
Badaru ya fadi hakan ne a yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida a wani taron manema labarai na Bikin Ranar Tunawa da Dakarun Soji na 2026 da aka yi a ranar Laraba a Abuja.

12 Nov, 2025
‘Yan wasan Super Eagles sun ƙaurace wa atisaye kan rashin biyansu alawus
Da yake tabbatar da lamarin kyaftin ɗin Super Eagles, Willam Troost-Ekong, ya ce da zarar an warware matsalar, su da kansu za su sanar da hakan.

12 Nov, 2025
An kama hodar ibilis mai nauyin kilogiram 1,000 a Nijeriya
Nijeriya da Amurka da Birtaniya suna aikin bincike a kan koken ɗin da kuɗinta ya kai dala miliyan 235 da aka kama a tashar jiragen ruwa ta Legas.

11 Nov, 2025
Jiragen yaƙin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan ISWAP da ɓarayin daji a Borno da wasu jihohin Arewa
Rundunar sojin saman Nijeriya ta ce nasarar da ta samu a Borno da Kwara da Katsina da wasu yankunan arewa maso yammacin ƙasar ta nuna sabunta matsa ƙaimi wajen daƙile ta’addanci bayan umarnin babban hafsan sojin saman ƙasar, Air Marshal Sunday Aneke

10 Nov, 2025
Babu abin da za mu rasa idan Nijeriya ta daina hulɗa da Amurka – Sheikh Gumi
“Akwai ƙasashe da suke rayuwa waɗanda ba su san akwai wani abu Amurka ba, wannan ƙasar ba ta nuna mana tana ƙaunarmu ba, sai dai ta tatse manmu, ta raba mu, ta cutar da mu,” in ji fitaccen malamin.

10 Nov, 2025
Damuwa kan kutsawar ‘yan bindiga Jihar Kano
Jihar Kano na daya daga cikin jihohin arewacin Nijeriya wadanda ake da zaman lafiya da kwanciyar hankali, idan aka kwatanta da sauran yankin da matsalar tsaro ta yi kamari.

10 Nov, 2025
Rundunar sojin Nijeriya ta ce ta kuɓutar da mutum 86 da Boko Haram ta yi garkuwa da su
Da dakarun operation Hadin Kai suka sami labarin, sai suka yi ta kan ‘yan ta’addan a inda suke a hanyar Mangari inda mayaƙan suka tsere a gigice.



