Gwamnatin Nijeriya ta amince a ci bashin dala 396 domin inganta kiwon lafiya da ayyukan jinƙai

Ministan Kuɗi na Nijeriya Wale Edun, ne ya bayyana amincewar da aka yi na cin bashin inda ya ce za a yi amfani da shi wurin tallafa wa mutanen da rikici ya raba da muhallansu da kuma aikin aiwatar da inganta cibiyoyin kiwon lafiya a Jihar Sokoto.
7 Nov, 2025
An gabatar da kudiri a Majalisar Dokokin Amurka don saka wa Ƙungiyoyin Miyetti Allah takunkumi

Kudirin ya ambaci kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) da Miyetti Allah Kautal Hore a matsayin kungiyoyin da ke da hannu a irin waɗannan laifuka.
6 Nov, 2025
Majalisar Dattawan Nijeriya ta amince a ɗaure malaman makaranta shekara 14 kan cin zarafin ɗalibai

Majalisar dattawana Nijeriya ta ce ƙudurin dake da manufar kare ɗalibai daga dukkan wani nau’in cin zarafi a makarantin gaba da sakandare.
6 Nov, 2025
An kashe ‘yan ta’adda fiye da 592 a Borno tun daga Maris din 2025 – Ministan Yada Labaran Nijeriya

Ministan yaɗa labarai na Nijeriya, Muhammed Idris ya ce gwamnatin Nijeriya tana yin nasara a yaƙinta da ta’addanci, inda ake samun manyan cigaba a arewa ta tsakiyar ƙasar.
5 Nov, 2025

Amurka na da ajanda a Nijeriya tana fakewa da yi wa Kiristoci kisan kare dangi – Sheik Bala Lau

China na adawa da Trump kan amfani da ‘addini da ‘yancin ɗan’adam’ domin tsoma baki a Nijeriya

Naira da hannayen-jari Nijeriya sun faɗi sakamakon barazanar da Trump ya yi ta kai hari ƙasar

Jami’an tsaron Nijeriya sun hallaka ‘yan bindiga 19 a Jihar Kano

Yadda barazanar da Trump ya yi kan aika sojoji Nijeriya ta tayar da ƙura
3 Nov, 2025
Dakarun Nijeriya sun kuɓutar da mutanen da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su Jihar Kogi
Sanarwa ta ce da dakarun sun samu bayanai game da aika-aikar ɓarayin dajin, sai suka nufi inda suke a dajin Achigili da ke Jihar Kogi.

2 Nov, 2025
Muna shirin ɗaukar mataki kan Nijeriya – Sakataren Ma’aikatar Yaƙi na Amurka
“Na’am, ranka ya daɗe. Kashe Kiristoci marasa laifi a Nijeriya — da ko’ina — dole ne ya ƙare nan da nan,” in ji Hegseth.

2 Nov, 2025
Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta soma shirin yiwuwar kai hari Nijeriya
Trump ya ce muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, dakarun ƙasarsa za su shiga cikin ƙasar cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ‘yan ta’adda masu kaifin kishin Musulinci.

1 Nov, 2025
Tinubu ya mayar da martani bayan Amurka ta ce ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Nijeriya
Shugaban ƙasar ya ce, duk wani bayani da ke nuna cewa Nijeriya ƙasa ce mai fama da tsatsauran ra’ayin addini, ba ya nuna ainihin gaskiyar abin da ke faruwa, kuma ba ya la’akari da ƙoƙarin gwamnati wajen tabbatar da ‘yancin addini da ra’ayi ga kowa.

1 Nov, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta sake jaddada kudirinta na yaƙi da tsatsauran ra’ayi
Gwamnatin ta yi jaje ga duk wanda ya rasa rayuwarsa sakamakon hare-haren ‘yan ta’adda, tare da yaba wa dakarun sojojin Nijeriya saboda jajircewarsu wajen kare ƙasar daga makiya.

1 Nov, 2025
Samaila Bagudo: ‘Yan bindiga sun sace Mataimakin Kakakin Majalisar Jihar Kebbi
Rundunar ‘yan sandan Nijeriya ta tabbatar da sace ɗan majalisar inda ta ce ‘yan bindiga ɗauke da makamai sun afka gidan ɗan majalisar da ke Ƙaramar Hukumar Bagudo inda suka sace shi jim kaɗan bayan ya kammala Sallar Isha’i.

1 Nov, 2025
Donald Trump ya ayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ake yi wa Kiristoci kisan gilla
Trump ya ɗauki matakin ne duk kuwa da cewa kwanakin baya mai ba shi shawara kan harkokin Afirka, Mossad Bullos, ya yi watsi da iƙirarin da ke cewa ana yi wa Kiristoci kisan kiyashi a Nijeriya.

31 Oct, 2025
‘Yan sandan Nijeriya sun ceto ‘yan kasashen waje 23 da aka yi garkuwa da su
Samamen ya biyo bayan wani rahoto da aka samu ne cewa an yaudari wasu ‘yan kasashen waje aka shigo da su Nijeriya da nufin za a samar musu ayyuka masu kyau, amma da isowarsu sai aka yi garkuwa da su.

31 Oct, 2025
EFCC ta tilasta wa boka dawo da gidaje da motocin da ya damfari wani mutum a Nijeriya
Kayayyakin sun hada da gidaje guda uku, da motoci na alfarma guda biyu da kuma kudi lakadan har naira miliyan daya da dubu dari daya na kafin alkalami, kamar yadda EFCC ta bayyana a shafinta na X.

31 Oct, 2025
An yi gagarumin garambawul ga rundunar sojojin ƙasa ta Nijeriya
Mai magana da yawun sojin ƙasa ta Nijeriya, Appolonia Aneke, ce ta sanar da sabbin naɗe-naɗen a wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis.



