An kashe mutum 2 a Taraba kan shugabancin masallacin Jumma’a

Jaridun Nijeriya sun ambato wata majiya daga garin da ke cewa rikicin ya ɓarke ne tsakanin Musulman garin kan wanda zai ja sallah a babban masallacin garin.
30 Oct, 2025
Tinubu ya cire sunayen masu manyan laifuka daga jerin wadanda ya yi wa afuwa

Afuwar da Shugaban Kasar ya yi wa mutum 175 da kotuna suka yanke wa hukunci kan laifukan da suka aikata, ta jawo ce-ce-ku-ce sosai a fadin kasar.
29 Oct, 2025
Mutum 170 sun shigar da bukatar neman zama ‘yan Nijeriya – Ministan Harkokin Gida

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wajen wani taro na Kwamitin da ke ba da shawara kan ba da shaidar zama ‘yan Nijeriya da aka gudanar a Abuja.
29 Oct, 2025
Gwamnatin Amurka ta soke bizar Wole Soyinka ta haramta masa shiga kasar

“Ba ni da biza; an haramta min shiga Amurka, Don haka idan kuna son ganina, kun san inda za ku same ni,” in ji Soyinka.
28 Oct, 2025

An lalata wani turken rarraba lantarki na Gombe zuwa Damaturu a Nijeriya – TCN

Gwamnatin Nijeriya ta karɓi ‘yan ƙasar 150 da suka maƙale a birnin Agadez na Nijar

‘Yan sandan INTERPOL sun kama ‘manyan mambobin ƙungiyoyin ta’addanci’ 11 a Nijeriya

Shugaba Tinubu ya sauya Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Dakarun Hadin Gwiwa sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda da dama a wurare daban-daban a Nijeriya
23 Oct, 2025
Dangote na shirin sayar da kashi 10 cikin 100 na hannayen-jarin matatar mansa
Dangote ya ce kamfanin man Nijeriya NNPC zai iya ƙara yawan hannayen-jarinsa a matatar bayan ya rage su zuwa kashi 7.2 cikin 100, amma sai mataki na gaba na haɓaka matatar ya kankama.

23 Oct, 2025
Jihohin Ondo da Kogi sun nemi a kwantar da hankali kan rahoton yiwuwar hare-haren ISWAP
Gwamnatocin sun ce hukumomin tsaro sun fara ɗaukar matakai na daƙile hare-haren da ƙungiyar ta’addancin ta shirya.

22 Oct, 2025
Haɗin kan gwamnonin Jigawa da Kano da Kaduna kan samar wa jihohinsu isasshiyar wutar lantarki
Bayanai sun ce gwamnatocin uku za su kafa wani asusu da za su saka naira biliyan hamsin a kamfanin na (FEA).

22 Oct, 2025
Hatsarin tankar dakon mai ya kashe aƙalla mutum 38 a Jihar Neja ta Nijeriya
Ganau sun ce waɗanda lamarin ya shafa suna kwasar man da ke gudana daga tankar man da ta faɗi ne a lokacin da lamarin ya haddasa gagarumar gobara da ta mamaye mutane.

21 Oct, 2025
Gwamnan Bauchi ya tabbatar da ƙirƙirar sabbin masarautu 13 da hakimai 111 a jihar
Tun mako biyu da suka wuce ne kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Alhaji Hamza Koshe Akuyam ya miƙa wa gwamnan cikakken rahoton aikin da ya saka su.

21 Oct, 2025
EFCC ta ƙwato naira biliyan 500 tare da samun mutum 7,000 da laifi cikin shekara biyu — Tinubu
Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa gwamnatinsa ba ta saka baki a ayyukan hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa ko ɓangaren shari’a ba, yana mai cewa an bai wa dukkansu biyu damar ayyukansu yadda kundin tsarin mulki ya tanada.

20 Oct, 2025
An kashe jami’ai a harin Boko Haram da sojoji suka daƙile a Jihar Borno
Wata sanarwa da Muƙaddashiyar Daraktar Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ta Rundunar Sojan Nijeriya Laftanal Kanal Appolonia Anele ta fitar a ranar Litinin ta ambaci sunan kwamandan a matsayin Laftanal Kanal Aliyu Paiko.

20 Oct, 2025
Gwamnatin China ta yaba wa Nijeriya kan ceto ‘yan ƙasarta huɗu da aka yi garkuwa da su
Rahotanni sun ce ‘yan bindiga ne suka yi wa masu haƙar ma’adinai na ƙasar China kwanton-ɓauna a hanyar zuwa wani wurin haƙar ma’adinai da ke ƙauyen Saminaka na Jihar Kogi.

20 Oct, 2025
‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijeriya a Jihar Borno
Bayanai sun nuna cewa mayaƙan Boko Haram sun kashe kwamandan soji na runduna ta 202 da ƙananan sojoji biyar da ‘yan Civilian Joint Task Force (JTF) guda uku a ƙauyen Kashimiri na ƙaramar hukumar Bama a wani harin kwanton-ɓauna da suka kai musu.

19 Oct, 2025
Wajibi ne ɗalibai su ci Darasin Lissafi a jarrabawar kammala sakandare – Gwamnatin Nijeriya
A ‘yan kwanakin nan ma’aikatar ilimi ta ƙasar ta ce za a daina tilasta wa ɗaliban da ke shirin karatun ɓangaren Arts cin darasin Lissafi, lamarin da ya jawo suka daga masana a ɓangaren ilimi waɗanda ke cewa hakan zai ƙara lalata ƙwazon ɗalibai.



