An kashe mutum 17 a yankin Birnin Gwari na Jihar Kaduna sakamakon arangama da ‘yan bindiga

Tashin hankalin ya fara ne a lokacin da wani gawurtaccen shugaban ɓarayin daji ya yi ƙoƙarin ƙwatar zinari daga hannun masu haƙar ma’adinai ta hanyar yi musu barazana da bindiga.
18 Oct, 2025
Kotu ta samu ‘yan China da Malaysia 59 da laifin intanet a Nijeriya

‘Yan ƙasashen ƙetaren da aka bayyana a matsayin ‘yan ƙasar China da ‘yan ƙasar Malaysia, suna cikin mutum 130 da aka kama a wani samame da ‘yan sanda suka kai wani gini a unguwar Jahi da ke birnin Abuja ranar 3 ga watan Nuwamba na shekarar 2024
17 Oct, 2025
Muhimman abubuwan da taron Malaman Musulunci na Nijeriya na Kaduna ya mayar da hankali a kai

Malamai daga ƙungiyoyin Musulunci daban-daban da sarakuna da ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki ne suka halarci taron, wanda maƙasudinsa shi ne haɗa kai don ɗaukar matakan magance matsalar tsaro da ke ta’azzara da ta tattalin arziki a yankin
16 Oct, 2025
Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta kama fatun jakuna da aka yi yunƙurin fasa-ƙaurinsu zuwa China

Hukumar ta kwastam ta kuma ƙwace man fetur da ƙwayoyi da aka yi yunƙurin safarar su a kan iyakar ƙasar da Kamaru.
16 Oct, 2025

Hauhawar farashi a Nijeriya ta ragu da kashi 2.1 a watan Satumba – NBS

Sabon reshen Boko Haram ‘Wulowulo’ na aika-aika a yankin tsakiyar Nijeriya — Gwamnan Nasarawa

‘Yan sandan Nijeriya sun kama masu safarar ƙwaya 105 a Jigawa

Majalisar Dokokin Nijeriya ta ba da shawarar yin manyan zaɓukan ƙasar a watan Nuwamban 2026

Majalisar Shura ta Kano ta zauna da Malam Lawan Triumph don jin bahasi
12 Oct, 2025
ASUU: Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya ta shiga yajin aikin gargaɗi
Shugaban ƙungiyar Farfesa Chris Piwuna ne ya sanar da hakan a lokacin wani taron manema labarai da aka gudanar a Jami’ar Abuja, a ranar Lahadi.

11 Oct, 2025
Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda tara, sun ceci mutum biyu da aka yi garkuwa da su a Borno
Dakarun Operation Hadin Kai da ke aiki a arewa maso gabashin Nijeriya ne suka samu wannan nasara inda suka kashe ‘yan ta’addan a samame daban daban da suka kai.

10 Oct, 2025
Mutum 26 da ake zargi da garkuwa da mutane sun shiga hannun ‘yan sanda a Kaduna
Kamen ya biyo bayan wasu samamen da jami’an ‘yan sandan da ‘yan sa kai suka kai tsakanin 3 da 5 ga watan Oktoba na shekarar 2025, inda suka mayar da hankali kan ƙungiyoyin da ke aika-aika a ƙananan hukumomin Anchau da Ikara da kuma Makarfi.

10 Oct, 2025
Tinubu ya yi wa Mamman Vatsa, Farouk Lawan da wasu mutum 173 afuwa
Tinubu ya ce ya ɗauki matakin yafe musu ne bayan masu laifin sun nuna nadamarsu da kuma shirinsu na sake komawa cikin al’umma don ci gaba da rayuwa.

9 Oct, 2025
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya naɗa Farfesa Joash Ojo Amupitan a matsayin shugaban INEC
Farfesa Amupitan shi ne zai maye gurbin Mahmood Yakubu a matsayin shugaban hukumar INEC.

9 Oct, 2025
Sojojin Nijeriya sun ceto kuɓutar da 37 da aka yi garkuwa da su, sun kashe ‘yan ta’adda 9
Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa haɗakar sojojin ƙasa na Nijeriya da wasu dakarun ƙasar sun kashe ‘yan ta’adda tara, tare da kama mutum 8 da ake zargi da laifuka, da ƙwato manyan makamai.

9 Oct, 2025
Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan ƙaruwar talauci a Nijeriya
“Dole a yi taka-tsan-tsan wajen fassara alƙaluman Bankin Duniya kai-tsaye,” in ji Sunday Dare, mai bai wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan watsa labarai.

8 Oct, 2025
‘Yan Majalisar Wakilan Nijeriya sun soki kudirin Majalisar Amurka kan zargin kisan Kiristoci
‘Yan majalisar sun ce Nijeriya ba ta fuskantar rikicin addini, inda suka bayyana buƙatar ɗaukar matakin diflomasiyya.

8 Oct, 2025
Geoffrey Nnaji: Ministan Kimiyya da Fasaha na Nijeriya ya yi murabus kan takardar digiri ta bogi
Daga baya jami’ar ta ce duk da cewa ministan ya fara karatu a jami’ar, a shekarar 1981, bai kamalla karatun digirin ba.

7 Oct, 2025
Gwamnatin Nijeriya ta ƙaddamar da shirin rigakafin ƙyanda da polio domin amfanar yara miliyan 16
Manufar wannan shiri ita ce a kawar da ciwon ƙyanda zuwa shekarar 2030, ta hanyar ƙarfafa rigakafin yara na yau da kullum, inganta bincike da sa ido kan ɓarkewar cuta, da kuma samar da shirye-shiryen kawar da ƙyanda a asibitoci na matakin farko.



