Jami’an tsaron Nijeriya sun kama shugabannin ƙungiyar ‘yan ta’adda ta Ansaru, Abu Barra da Mamuda

“Nijeriya ta daɗe tana neman waɗannan mutanen biyu ruwa-a-jallo, haka kuma ‘yan ta’adda ne da ƙasashen duniya ke nemansu,” a cewar Malam Nuhu Ribadu.
16 Aug, 2025
Babban Hafsan Tsaron Nijeriya ya kare yadda sojoji ke tunkarar masu tayar da ƙayar baya

Sojojin Nijeriya na ƙara amfani da hare-haren sama kan ƙarin barazanar ‘yan bindiga a yankunan arewaci da tsakiyar ƙasar.
15 Aug, 2025
Amurka ta amince a sayar wa Nijeriya makamai da bamabamai da rokoki da suka kai naira biliyan 532

Tuni hukumar DSCA mai kula da tsaron Amurka tare da manufofin ƙasashen wajen ƙasar ta miƙa takardun shaidar da ake buƙata don sanar da Majalisar Dokokin Amurka game da yiwuwar sayar da makaman.
14 Aug, 2025
Boko Haram: Sojojin Saman Nijeriya ‘sun kashe ‘yan ta’adda 592’ a Borno cikin wata takwas

Rundunar ta ce hare-haren, waɗanda suka ƙunshi tashin jiragen yaƙi sau 798, sun yi nasarar rage ƙarfin mayaƙan ISWAP da Boko Haram sosai a arewa maso gabashin Nijeriya.
13 Aug, 2025

Abin da ya sa EFCC ta kama tsohon gwamnan Sokoto Aminu Tambuwal

Sojojin Nijeriya ‘sun kashe fiye da ‘yan bindiga 100’ a wasu hare-hare a Zamfara

EFCC ta yi ƙarin haske kan samamen da ta kai Obasanjo Presidential Library

An yi zanga-zanga a Zamfara kan sabbin hare-haren ‘yan bindiga

Sojojin Nijeriya sun tarwatsa bikin ‘yan ta’adda, sun kashe 30 a jihar Zamfara
7 Aug, 2025
Shugaban EFCC ya ƙaryata rahoton da ke cewa ya tilasta wa shugaban NNPC yin murabus
Wasiƙar da lauyan shugaban EFCC, Olatimbo Ayinde, ya aika wa People Gazette ta yi gargaɗin cewa idan jaridar ba ta janye labarin kuma ta nemi afuwa ba, shugaban hukumar zai ɗauki maka ta a kotu.

6 Aug, 2025
Tinubu ya ba da umarnin hanzarta ƙaddamar da kiwon lafiya kyauta ga ‘yan fansho a Nijeriya
Shirin zai gudana ne ƙarƙashin Tsarin Karo-karon Fansho na ƙasa.

6 Aug, 2025
Ambaliyar shekarar 2025: Mutum 191 sun mutu, 94 sun ɓata a Nijeriya – NEMA
Bayanan shekarar 2025 na hukumar NEMA sun nuna cewa ambaliyar ruwan ta fi shafar yara da mata.

5 Aug, 2025
NAFDAC ta ƙwace haramtattun kayayyaki na ₦1.5b da wa’adinsu ya ƙare a kasuwar bajekoli ta Legas
Wata sanarwa da hukumar ta NAFDAC ta wallafa a shafinta na X ta ce an gudanar da aikin ne karkashin jagorancin Daraktan bincike da tilastawa na hukumar, Martins Iluyomade.

5 Aug, 2025
Dakarun Nijeriya sun kashe ‘yan ta’addan Boko Haram 17 a Borno
Ya ce dakarun masu jajircewa sun gano tare da fasa bama-bamai sama da 14 da ‘yan ta’addan suka ɗana a wurare daban daban.

4 Aug, 2025
Hukumar Kwastam ta Nijeriya ta kwace tsuntsaye masu rai 1,620 da aka yi niyyar kai su Kuwait
Tsuntsayen masu rai fiye da 1,620 sun haɗa da nau’ukan kanari da aku da sauran su.

4 Aug, 2025
NiMet ta yi hasashen ruwan sama babu ƙaƙƙautawa na kwana uku a faɗin Nijeriya daga ranar Litinin
Hasashen na kwanaki uku da aka fitar a Abuja ranar Lahadi, na zuwa ne bayan ruwan sama ya lalata gidaje kimanin 50 da gonaki da wuraren ibada a Jihar Filato.

4 Aug, 2025
NDLEA ta kama miyagun ƙwayoyi da aka ɓoye a cikin jan-baki, madubin mota da takalma
NDLEA ta ce jami’anta a filin jirgin saman Legas sun cafke wasu kaya da aka yi niyyar kaiwa Libreville, Gabon, inda aka ga ƙwayoyin Tramadol 57,420 (225mg) da kuma hodar iblis ƙulli 57 da nauyinsu ya kai kilo 1.60 da aka ɓoye a cikin madubi 71.

3 Aug, 2025
‘Yan bindiga sun sace fiye da mutum 50 a Jihar Zamfara
Wannan na zuwa ne ƙasa da mako guda bayan ‘yan bindigan a Zamfara da ke arewacin Nijeriya sun kashe mutum 33 da suka yi garkuwa da su tun a watan Fabrairu duk da samun kuɗin fansa na naira miliyan 50 da suka yi.

3 Aug, 2025
Ma’aikatan jinya a Nijeriya sun dakatar da yajin aikin gargaɗi
Wata sanarwa da ƙungiyar National Association of Nigeria Nurses and Midwives ta fitar ta ce gwamnati ta saurari ƙorafinsu kuma ta faɗi “lokacin” da za ta cika alƙawuran da ta ɗauka, sai dai ta ce za ta sanya ido sosai don ganin ko za ta ɗauki mataki



