25 May, 2025

Jami’an tsaron Nijeriya sun kashe masu garkuwa da mutane 21 a dajin Katsina

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Katsina, Nasiru Muazu ya ce jami’an rundunar “Forest Sanity III” sun halaka masu garkuwa da mutane aƙalla 21 inda wasu kuma suka tsere da raunuka a jikinsu.

2025 03 26t094549z 1530292391 rc2wkda7zmrv rtrmadp 3 nigeria security

23 May, 2025

Sojojin Nijeriya sun kashe ‘yan Boko Haram 16 a Damboa na jihar Borno

A wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X, ta ce lamarin ya faru ne a lokacin da ‘yan ta’addar Boko Haram ɗin suka yi ƙoƙarin kutsawa garin don kai hari.

hadin 20kai

23 May, 2025

Gwamnatin Tinubu ta samu nasara kan matsalolin tsaron da ta gada daga gwamnatin baya – Ribadu

Mallam Nuhu ya ce ta hanyar haɗin gwiwa da jami’an tsaro suka yi, an daƙile ta’asar da ake yawan aikatawa waɗanda suka haɗa da kashe-kashen jama’a da lalata wurare da sace-sacen jama’a da kuma hare-haren ta’addanci a kan cibiyoyin gwamnati.

477305141 1141809304070939 2444864462183842699 n

21 May, 2025

Akwai masu kwarmata bayanai wa Boko Haram cikin ‘yan siyasa da sojoji – Gwamna Zulum

“Ba zan iya cewa ɗari bisa ɗari duk waɗanda suka miƙa wuya suna abin da ya dace ba, amma ina son in tabbatar muku cewa sama da kashi 99 cikin 100 suna abin da ya dace kuma ba su da hannu a cikin ta’addanci,” in ji Zulum

ey7vxdgxeaij0an

21 May, 2025

EFCC ta mika gidaje 753 da aka ƙwace daga Emefiele ga Ma’aikatar Gidaje ta Nijeriya

A cikin watan Afrilun shekarar 2025 ne dai wata kotun birnin Tarayyar Nijeriya, Abuja ta kori ƙarar da Emefiele ya shigar ta neman a soke ƙwace gidajen domin ba a ba shi damar kare kansa game da mallakar gidajen.

gra3irtx0aeiprg

19 May, 2025

‘Yan bindiga sun kashe mutum 50 a jihohi uku na arewacin Nijeriya a kwana biyu

‘Yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 50 a hare-hare daban-daban da suka kai a jihohi uku na arewacin Nijeriya.

21459239 0 112 1080 608 main

19 May, 2025

Hukumar tace fina-finai ta Jihar Kano ta dakatar da nuna wasu fina-finai masu dogon zango 22

Hukumar, ta ce ta yi hakan ne a ƙoƙarinta na tabbatar dacewa ana bin dokar tace fina-finai sau da ƙafa tare da ƙara ɗora masana’antar Kannywood a kan saiti.

abba

19 May, 2025

Gwamnan Borno ya roƙi gwamnatin Tarayyar Nijeriya kar ta bari Boko Haram ta ƙwace garin Marte

Zulum, wanda da shi aka yi ta tsare-tsaren ayyukan tsaro har cikin tsakar dare a ranar Asabar, ya gudanar da rangadi don tantance ƙalubalen da aka fuskanta a Marte, tare da lalubo hanyoyin da za a bi don samar da zaman lafiya.

ey7vxdgxeaij0an

17 May, 2025

Gwamnatin Kano ta haramta bikin ‘ƙauyawa day’ da soke lasisin gidajen bukukuwa

Shugaban hukumar tace fina-finai ta Kano Abba El-Mustapha ya ce sun samu ƙorafi daga jama’ar gari da malamai da ‘yan kasuwa wanda hakan ya sa aka haramta wannan biki.

484854872 1053799600113628 5282398829110682128 n

16 May, 2025

Za mu ci gaba da karya farashin shinkafa —Shugaban BUA

Shugaban kamfanin BUA ya yaba wa Shugaba Bola Ahmad Tinubu kan damar shigowa da abinci da ya bayar, inda ya ce “hangen nesansa” ya taimaka wajen karya farashin abinci a ƙasar.

484798313 1053626223458023 300324107043152458 n
Ana lodawa...