Afirka

Sojojin Sudan sun sake ƙwace muhimman wurare daga dakarun RSF a El-Fasher

Wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce dakarunta sun kai farmaki a wurare daban-daban da ke hannun mayaƙan RSF a El-Fasher inda suka sanya su yin asarar dakaru da kayayyakin aiki.

Newstimehub

Newstimehub

8 Oct, 2025

1759754845578 4wzqce adce5224e7c6f1c8ae531e556b38ac4412ca99f10eb55e03c5befac2530573db

Rundunar sojin Sudan ta ce ta ƙwato yankuna da dama da ke ƙarƙashin mayaƙan rundunar ko-ta-kwata ta Rapid Support Forces (RSF) a El-Fasher, babban birnin Jihar North Darfur da ke yammacin Sudan.

Wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce dakarunta sun kai farmaki a “wurare daban-daban” da ke hannun mayaƙan RSF a El-Fasher inda suka sanya su yin asarar dakaru da kayayyakin aiki.

Kazalika rundunar sojin ta ce dakarun nata sun ƙwace motocin yaƙi da dama, ko da yake ba ta faɗi adadinsu ba, amma ta ƙara da cewa sun lalata motocin yaƙi shida, ciki har da motoci masu sulke.

A cewar rundunar sojin, mayaƙan RSF sun ƙaddamar da hari a kudacin El-Fasher, amma sojojin gwamnati sun daƙile harin sannan suka haddasa musu asara mai yawa.