Rundunar sojin Sudan ta ce ta ƙwato yankuna da dama da ke ƙarƙashin mayaƙan rundunar ko-ta-kwata ta Rapid Support Forces (RSF) a El-Fasher, babban birnin Jihar North Darfur da ke yammacin Sudan.
Wata sanarwa da rundunar sojin Sudan ta fitar ta ce dakarunta sun kai farmaki a “wurare daban-daban” da ke hannun mayaƙan RSF a El-Fasher inda suka sanya su yin asarar dakaru da kayayyakin aiki.
Kazalika rundunar sojin ta ce dakarun nata sun ƙwace motocin yaƙi da dama, ko da yake ba ta faɗi adadinsu ba, amma ta ƙara da cewa sun lalata motocin yaƙi shida, ciki har da motoci masu sulke.
A cewar rundunar sojin, mayaƙan RSF sun ƙaddamar da hari a kudacin El-Fasher, amma sojojin gwamnati sun daƙile harin sannan suka haddasa musu asara mai yawa.














