Gabas Ta Tsakiya

Ƙasashen Afirka Sun Ɗauki Matakan Gaggawa Domin Kare ’Yan Ƙasarsu Yayin Rikicin Gabas Ta Tsakiya

Ƙasashen Afirka sun fara ɗaukar matakan kariya da gargadi ga ’yan ƙasarsu yayin da rikicin Iran, Isra’ila da Amurka ke barazana ga tsaro da tattalin arzikin duniya.

Newstimehub

Newstimehub

2 Mar, 2026

lebanon israel iran us 44540

Yayin da rikicin Iran, Isra’ila da Amurka ke ƙara tsananta, wasu gwamnatocin Afirka sun fara ɗaukar matakan kariya cikin gaggawa domin tabbatar da lafiyar ’yan ƙasarsu da ke yankin. Tashin hankalin, wanda ya biyo bayan hare-haren haɗin gwiwar Amurka da Isra’ila kan Iran da kuma martanin da Tehran ta mayar, ya haddasa rufe sararin samaniya da tangarda a zirga-zirgar jiragen sama na duniya.

Afirka ta Kudu ta buƙaci duk ’yan ƙasarta da ke Gabas ta Tsakiya su yi rajista da ofisoshin jakadanci domin a san inda suke, tana mai gargaɗin cewa rufe sararin samaniya ya bar wasu a makale. Uganda ta shawarci ’yan ƙasarta da ke Iran su bar ƙasar idan zai yiwu, tare da janye wasu ma’aikatan jakadancinta. Ghana kuma ta dakatar da zirga-zirgar da ba ta da muhimmanci zuwa yankin, tana gargadin cewa haɗarin zirga-zirgar sama da teku ya ƙaru.

Kenya ta fitar da gargadin tsaro ga ’yan ƙasarta a Iran, Isra’ila da wasu ƙasashen Gulf, tana shawartar su guji wuraren soja da taron jama’a masu yawa. A matakin nahiyar, Tarayyar Afirka ta yi kira da a tsagaita wuta tare da komawa tattaunawa, tana gargaɗin cewa tsawaita rikicin na iya dagula kasuwannin makamashi da samar da abinci, musamman ga ƙasashen Afirka da ke fuskantar matsin tattalin arziki.

Ana kuma nuna damuwa kan yiwuwar toshe Mashigin Hormuz, wata muhimmiyar hanya ta jigilar mai a duniya, wanda hakan ka iya shafar tattalin arzikin Afirka da ke dogaro da farashin makamashi mai daidaito.

Majiyar Labari: TRT HAUSA