Sabbin rahotanni sun nuna cewa Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta sanar da ƙarshen tsayuwarta ta soja a Yemen, tana mai cewa matakin ya biyo bayan ƙarin tashin hankali da kuma buƙatar kare lafiyar sojojinta. Ma’aikatar Tsaron UAE ta ce an janye ragowar tawagar yaƙin yaƙi da ta’addanci ne cikin natsuwa tare da haɗin gwiwar abokan hulɗa domin tabbatar da tsaro.
Tun kafin wannan mataki, Shugaban Majalisar Jagorancin Yemen, Rashad al-Alimi, ya soke yarjejeniyar tsaro da UAE tare da ba ta awanni 24 ta janye, sannan ya ayyana dokar-ta-baci na tsawon kwanaki 90 tare da kulle filayen jirage da iyakoki na tsawon sa’o’i 72. Wannan ya faru ne bayan dakarun ƙawancen Saudiyya sun kai hari kan wasu jiragen ruwa da ake dangantawa da UAE a tashar jiragen ruwa ta Mukalla, yayin da tashin hankali ke ƙaruwa tun bayan Southern Transitional Council (STC) ta kwace wasu yankuna a gabashin Yemen.














