Turkiyya

Erdogan ya yaba da juriyar al’ummar Falasɗinu duk da wahalhalu

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya yaba da juriyar al’ummar Falasɗinu, yana sukar Isra’ila kan hana shigar da agajin jin ƙai zuwa Gaza.

Newstimehub

Newstimehub

9 Jan, 2026

download 2 4

Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya jinjina wa al’ummar Falasɗinu kan yadda suke ci gaba da nuna juriya da ƙwazo duk da matsanancin halin da suke ciki.

Erdogan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wani taron bayar da kyaututtuka a Istanbul, inda ya ce Turkiyya ta yi ƙoƙarin tura agajin jin ƙai zuwa Gaza, har ta hannun Majalisar Ɗinkin Duniya, amma Firayim Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya hana hakan.

Ya zargi Netanyahu da sanya shinge ga shigar da taimakon jin ƙai, yana mai cewa wannan mataki na ƙara tsananta halin da fararen hula ke ciki a Gaza.

Tun daga watan Oktoban 2023, hare-haren Isra’ila sun kashe sama da Falasɗinawa 71,000, yawancinsu mata da yara, tare da jikkata fiye da 171,000. Duk da ayyana tsagaita wuta a watan Oktoba, rahotanni sun nuna cewa hare-haren sun ci gaba, inda aka kashe daruruwan mutane tare da jikkata dubban wasu.

Majiyar Labar: AA