Amurka ta kai muhimman kayayyakin soji ga Nijeriya don tallafawa ayyukan tsaro da kasar ke gudanarwa, wanda hakan ke karfafa dangantakar tsaro tsakanin kasashen biyu.
A cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin X, rundunar sojin Amurka ta Afirka (AFRICOM) ta ce sojojin Amurka sun kai kayayyakin ga abokan huldarta Nijeriya a Abuja, inda ta lura cewa isar da kayayyakin yana goyon bayan kokarin sojojin Nijeriya na yanzu kuma yana nuna muradun tsaro iri daya.
Amurka ta aika muhimman kayayyakin soji zuwa Nijeriya domin tallafa wa ayyukan tsaro da ƙasar ke gudanarwa, lamarin da ke nuna ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu. Rundunar Sojin Amurka ta Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da isar da kayan a Abuja, tana mai cewa matakin yana goyon bayan ƙoƙarin sojojin Nijeriya na yanzu tare da nuna muradun tsaro na bai ɗaya.
Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya ya amince da isar da kayayyakin, wanda ya zo ne kwanaki bayan hare-haren sama da Amurka ta kai a ranar Kirsimeti a jihar Sokoto, a wani aiki na haɗin gwiwa da nufin kai farmaki kan ‘yan bindiga da ake danganta su da ƙungiyar IS.
Hukumomi sun bayyana cewa harin da aka kai a ranar 25 ga Disamban 2025 ya nuna sabon mataki a haɗin gwiwar tsaro tsakanin Washington da Abuja, duk da cewa dangantakar kasashen biyu ta taɓarɓare a baya sakamakon wasu kalamai daga Shugaba Donald Trump game da matsalar tsaro a Nijeriya.
Nijeriya na ci gaba da fuskantar manyan ƙalubalen tsaro tun daga rikicin Boko Haram zuwa ayyukan ‘yan fashi da makami a arewacin ƙasar. Bayan warware saɓanin diflomasiyya, jami’an tsaro sun ce a nan gaba Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya za ta jagoranci ayyukan, yayin da Amurka za ta ba da tallafin leken asiri ta jiragen sama.














