Gabas Ta Tsakiya

‘Ko ba daɗe ko ba jima’: Ministan Isra’ila ya yi barazanar yaƙi ga Syria, yana sa ido kan Turkiyya

Ministan Kula da Harkokin ‘Yan Isra’ila Mazauna Ƙasashen Waje, Amichai Chikli, ya ce nan gaba Isra’ila za ta yi yaki da Syria, sannan ya ce Syria da Turkiyya sun fi Iran zama “babbar barazana da ƙalubale” ga Isra’ila.

Newstimehub

Newstimehub

18 Jun, 2026

5c6d3c32949aa53acb08e83acf8f311ee2e34f844d3a3db1a36167aac1ddba7e main

Ministan Kula da Harkokin ‘Yan Isra’ila Mazauna Ƙasashen Waje, Amichai Chikli, ya ce nan gaba Isra’ila za ta yi yaki da Syria, sannan ya ce Syria da Turkiyya sun fi Iran zama “babbar barazana da ƙalubale” ga Isra’ila.

“Za mu yi yaki da Syria, da wuri ko daga baya, domin ita da Turkiyya sun fi damun mu fiye da Iran,” in ji Chikli a ranar Alhamis a wata hira da rediyon Isra’ila 103FM, wanda ke haɗe da jaridar Maariv.

Sharhin nasa ya zo awanni kaɗan bayan Iran da Amurka sun sanya hannu kan wata yarjejeniya ta fahimta wadda nufinta shi ne kawo ƙarshen tashin hankali a fannoni da dama na yankin, ciki har da Lebanon.

Chikli, memba na jam’iyyar Likud mai mulki karkashin Firaminista Benjamin Netanyahu, ya sha yin suka ga wasu ɓangarorin yankin da ke shiga ƙoƙarin diflomasiyya don warware rikice-rikicen da ke ci gaba a Gabas ta Tsakiya.

Tsoron Isra’ila game da sabon daidaituwar yankin da ke tasowa

Ministan ya nuna damuwa kan abin da ya kira “tsagin Qatar-Turkiyya-Pakistan,” yana zargin cewa kasashen uku sun yi tasiri wajen samar da yarjejeniyar da ke bayyana tsakanin Washington da Tehran.

“Yarjejeniyar da ake yi tana damun mutane, kuma abin da ya fi damuna shi ne farfaɗowar tattalin arzikin Iran,’ in ji Chikli, yana nuni da tasirin yaƙi da shekaru na takunkumi kan Iran.

Ya ce babban abin damuwarsa shi ne wannan daidaituwar yankin da, a cewarsa, ta taimaka wajen tsara yarjejeniyar.

“Abin da muke gani a gaban idonmu shi ne tasowar wani sabon tsagi,” in ji Chikli, yana kwatanta shi da “tsagin Sunni mai tsananin haɗari da tsattsauran ra’ayi”.

Pakistan da Qatar sun taka rawa wajen shiga tsakani a tattaunawar da aka yi tsakanin Washington da Tehran, yayin da Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya maraba da yarjejeniyar Amurka da Iran, yana kiran ta “muhimmin ci gaba” don zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.