Nijeriya Tsaro

Sojojin Nijeriya Sun Hallaka ’Yan Ta’addan Lakurawa, Sun Ceto Mutane 62 a Kebbi da Zamfara

An gudanar da farmakin ne ta hanyar haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da ’yan sa-kai na yankin, abin da ke nuna kyakkyawar haɗin kai da ke tsakaninsu wajen yaƙi da ’yan ta’adda da ’yan bindiga, kamar yadda Laftanal Kanal Olaniyi Osoba ya bayyana.

Newstimehub

Newstimehub

22 Jan, 2026

75eb1001743337db6dcffa1a9e19628b04d50d1b6323b1537eac1128b32a7b9e main

Dakarun Sojin Nijeriya sun samu gagarumar nasara a yaƙin da suke yi da ’yan ta’adda a Arewa maso Yammacin ƙasar, bayan sun kashe wasu daga cikin ’yan kungiyar Lakurawa tare da kuɓutar da daruruwan mutanen da aka yi garkuwa da su, lamarin da ya kawo ɗan sauƙi ga al’ummomin da ke fama da hare-haren ’yan bindiga.

Rundunar Operation Fansan Yamma ta kashe ’yan ta’adda biyu a Jihar Kebbi, ta kuma kwato babura da kayan da suke amfani da su. Haka kuma, a wani samame a Dajin Munhaye na Jihar Zamfara, dakarun sun kai farmaki maboyar shugaban ’yan ta’adda Kachalla Alti, inda suka kuɓutar da mutane 62 da aka yi garkuwa da su.

Farmakan sun samu nasara ne sakamakon sahihan bayanan sirri da haɗin gwiwa tsakanin sojoji, jami’an tsaro da ’yan bijilanti na yankin.

Majiyar Labari: TRT HAUSA