Shugaban China, Xi Jinping, ya sanar da cewa daga 1 ga watan Mayu za a soke harajin kwastam kan kayayyakin da ke shigowa daga kusan dukkan ƙasashen Afirka. Rahotanni sun ce matakin ya zo ne a wani bangare na faɗaɗa manufofin kasuwanci da Beijing ke aiwatarwa da nahiyar.
Tun da farko, China ta riga ta cire haraji ga ƙasashen Afirka 33, kuma ta bayyana aniyar faɗaɗa tsarin zuwa yawancin ƙasashen nahiyar. Sabuwar sanarwar ta nuna cewa Eswatini kaɗai ba za ta ci gajiyar shirin ba, sakamakon dangantakar diflomasiyya da take da ita da Taiwan.
China, wadda ke matsayin babbar abokiyar kasuwanci ta Afirka, na ci gaba da ƙarfafa alaƙarta da nahiyar ta hanyoyi daban-daban, ciki har da zuba jari a ababen more rayuwa karkashin shirin Belt and Road. Masana na ganin matakin zai iya ƙara bunƙasa cinikayya tsakanin bangarorin biyu.
Sanarwar ta zo ne a lokacin da shugabannin Afirka ke taron AU, yayin da ƙasashe da dama ke neman sabbin hanyoyin kasuwanci bayan sauye-sauyen manufofin haraji a duniya.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














