A daidai lokacin da jama’a ke fatan samun kwanciyar hankali bayan bukukuwa a jihar Kebbi, rahotanni sun nuna cewa wasu hare-hare sun sake jefa al’umma cikin firgici. Mazauna yankin sun shiga jimami bayan asarar rayuka da dukiyoyi.
Kakakin ‘yan sandan jihar, Bashir Usman, ya shaida wa AFP cewa maharan sun kai farmaki ƙauyuka bakwai da ke gundumar Bui da misalin karfe 1:15 na rana a ranar Laraba. Ƙauyukan da abin ya shafa sun hada da Mamunu, Awasaka, Tungan Tsoho, Makangara, Kanzo, Gorun Naidal da Dan Mai Ago.
Wani rahoton tsaro ya nuna cewa an kashe fiye da mutum 30 yayin da mazauna yankunan suka yi yunkurin kare kansu. Haka kuma maharan sun sace shanu masu yawa kafin jami’an ‘yan sanda, sojoji da ‘yan sa-kai su isa wurin.
Hare-haren sun faru ne kwanaki bayan bikin kamun kifi na Argungu Fishing Festival wanda UNESCO ta sanya a jerin al’adun duniya.
Ana zargin kungiyar Lakurawa da kai hare-hare a arewacin Kebbi da makwabciyarta Sokoto, inda suke kai farmaki daga dazuzzuka tare da satar dabbobi da kakaba haraji ga mazauna.
Wasu masu bincike sun danganta kungiyar da Islamic State a yankin Sahel, duk da cewa ana ci gaba da muhawara kan hakan.
Halin tsaro a Nijeriya na ci gaba da kasancewa kalubale, inda rikice-rikice daban-daban ke addabar sassan kasar, ciki har da arewa maso gabas da arewa maso yamma.
Majiyar Labari: TRT HAUSA














