Gabas Ta Tsakiya

Iran Ta Ce Ta Kai Hare-Haren Ramuwar Gayya Kan Wurare 500 Masu Alaƙa Da Isra’ila Da Amurka

Iran ta ce ta kai hare-hare kan wurare 500 da ke da alaƙa da Isra’ila da Amurka, yayin da adadin mace-mace ke ƙaruwa a bangarorin biyu.

Newstimehub

Newstimehub

3 Mar, 2026

2026 03 01t132606z 1 lynxmpem2010s rtroptp 3 iran crisis israel

Rundunar Juyin Juya Halin Iran ta sanar a rana ta uku da fara yaƙin cewa ta kai hare-hare kan muhimman wurare 60 da kuma sama da wurare 500 da ke da alaƙa da Isra’ila da Amurka a Gabas ta Tsakiya.

A cikin sanarwar da ta fitar ranar Litinin, rundunar ta ce ta yi amfani da jirage marasa matuƙa sama da 700 tare da ɗaruruwan makamai masu linzami tun bayan fara rikicin.

Tehran ta ce hare-haren nata ramuwar gayya ne ga farmakin haɗin gwiwa da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar tun ranar 28 ga Fabrairu, wanda ya kashe Jagoran Addinin Iran, Ali Khamenei, tare da kai hari kan wurare da dama.

Wasu makamai masu linzami sun afka kai tsaye a Isra’ila, inda aka tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 11 tare da jikkatar wasu a wurare kamar Beit Shemesh da kusa da Birnin Ƙudus.

Iran ta kuma kai hari kan sansanonin sojin Amurka a yankin, inda rahotanni suka ce aƙalla jami’an soji huɗu sun mutu yayin da wasu suka jikkata. Ƙasashen Larabawa da ke ɗauke da sansanonin Amurka, ciki har da UAE, Kuwait, Qatar, Bahrain, Saudi Arabia da Oman, sun fuskanci hare-hare kan wuraren soji da na ababen more rayuwa.

A nata ɓangaren, rundunar sojin Amurka ta CENTCOM ta ce jami’anta 18 sun ji munanan raunuka tun bayan fara rikicin, yayin da aka tabbatar da mutuwar jami’i na huɗu sakamakon raunukan da ya samu. A Iran kuma, ƙungiyar Red Crescent ta ce hare-haren Amurka da Isra’ila sun kashe aƙalla mutum 555 a ƙananan hukumomi 131, ciki har da mummunan hari a Minab da ya yi sanadin mutuwar yara mata 180 a wata makaranta.

Majiyar Labari: TRT WORLD