Gabas Ta Tsakiya

Ben-Gvir ya sanar da shirin Isra’ila na gina sabbin haramtattun matsugunai a Lebanon

Ben-Gvir ya kuma yi barazanar kara tsauraran matakan da ya saka a kan Falasdinawan da ke daure a gidajen kurkukun Isra’ila.

Newstimehub

Newstimehub

15 May, 2026

2026 05 14t160056z 2028810686 rc239laheokm rtrmadp 3 israel palestinians jerusalem march

Ministan Tsaron Ƙasa na Isra’ila, Itamar Ben-Gvir, ya ce gwamnati na shirin kafa matsugunan da ba sa bisa ƙa’ida a Lebanon da kuma korar Falasdinawa daga Gaza da Gabar Yamma da aka mamaye.

Wannan kalami na zuwa ne a lokacin da Ben-Gvir ya halarci wani taro a Urushalima don tunawa da mamayar da Isra’ila ta yi wa Gabashin Urushalima, bisa ga kalandar Ibrananci, kamar yadda Channel 7 ta Isra’ila ta ruwaito a ranar Alhamis.

“Muna da ƙarin shirye-shirye don ƙarfafa ƙaura daga Gaza, ƙarfafa ƙaura daga Yahudiya da Samariya (Gabar Yamma da aka mamaye), da kuma gidaje a Lebanon, kuma ba za mu ji tsoron kawar da duk wanda ya tashi ya kashe mu ba,” in ji Ben-Gvir.

Isra’ila na ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza a kowace rana, tun daga watan Oktoban 2025, inda aka kashe aƙalla mutane 857 tare da raunata wasu 2,486.

Isra’ila ta ci gaba da karya yarjejeniyar tsagaita wuta a Lebanon, wadda za ta ci gaba har zuwa ranar 17 ga Mayu, inda ta kashe mutane 2,896 tare da raunata wasu 8,824 tun daga ranar 2 ga Maris.

Ben-Gvir ya kuma yi barazanar kara tsauraran matakan da ya saka a kan Falasdinawan da ke daure a gidajen kurkukun Isra’ila bayan ya yi nuni da dokar da ya gabatar a watan Maris, wadda ta ba da damar yanke hukuncin kisa ga fursunoni Falasdinawa.

Gidajen kurkukun Isra’ila “sun zama gidajen yari na gaske”, in ji shi.

“Babu alawa ko cakuleti, babu karatu, babu ajje kudi, babu talabijin ko rediyo. An bar su da mafi ƙaranci kawai.”

A ranar 30 ga Maris, Knesset ta Isra’ila ta amince da dokar da ta ba da damar kashe fursunonin Falasɗinawa da ƙuri’a 62, inda wasu 48 suka nuna kin amincewa,

Bayan jefa ƙuri’ar, Kwamitin Majalisar Dinkin Duniya kan Kawar da Wariyar Launin Fata ya yi kira ga Isra’ila da “nan take” ta soke dokar.

Dokar ta ba da izinin yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga fursunoni Falasɗinawa.

Dokar ta kuma ba da dama ga kotuna da su yanke hukuncin kisa ba tare da buƙatar mai gabatar da ƙara ba kuma ba tare da buƙatar yanke shawarar dukkan alƙalai ba, wanda hakan ya ba da damar amincewar alkalai ‘yan kadan marasa.

Fursunoni Falasɗinawa sama da 9,600, ciki har da yara da mata na tsare a gidajen yarin Isra’ila, inda suke fuskantar azabtarwa, yunwa, da kuma sakaci a fannin kula da lafiya wanda ya haifar da mutuwar mutane da dama, a cewar ƙungiyoyin kare haƙƙin Falasɗinawa da Isra’ila.