Afirka

‘Yan Boko Haram sun kashe sojojin Nijar, in ji kafar watsa labaran gwamnati

Kamfanin dillancin labaran gwamnatin Jamhuriyar Nijar ANP bai faɗi adadin sojojin da aka kashe ba, sai dai ya tabbatar da cewa an kashe sojoji a harin da aka kai a kusa da garin N’Guigmi da ke yankin Tafkin Chadi.

Newstimehub

Newstimehub

1 Aug, 2026

f438e0ac 1754 4ec4 8b4a c8aca37ab490 1780422303460

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun mutu a wani hari da ‘yanta’adda na Boko Haram suka kai musu a kudu maso gabashin ƙasar, a cewar kamfanin dillancin labaran gwamnatin ƙasar.

An kai harin ne ranar Jumma’a a kusa da garin N’Guigmi na Jihar Diffa da ke da iyaka da Nijeriya da Kamaru da kuma Chadi, inda ‘yanta’addan Boko Haram ke da sansanoni da dama, a cewar kamfanin dillancin labarai na ANP.

ANP bai faɗi adadin sojojin da aka kashe ba, sai dai ya tabbatar da cewa an kashe sojoji “sakamakon harin da ‘yanta’addan Boko Haram suka kai a wajen garin N’Guigmi”.

Ya ruwaito cewa gwamnan Jihar Diffa, Janar Mahamadou Ibrahim, ya ziyarci garin nan N’Guigmi domin yin jana’izar sojojin da aka kashe.

Amma kamfanin dillancin labarai na AFP ya ambato wasu majiyoyi suna cewa sojojin da aka kashe sun kai goma.

Ƙungiyar Boko Haram, wadda ta ƙaddamar da hare-haren ta’addanci a arewacin Nijeriya a shekarar 2009, ta kashe dubban mutane tare da raba miliyoyi da muhallansu.

Hare-haren ƙungiyar sun watsi zuwa Jamhuriyar Nijar da Kamaru da Chadi, lamarin da ya sa hukumomi suka kafa rundunar tsaro ta haɗin gwiwa domin shawo kan rikicin.