Sabon jawabin Shugaban Amurka Donald Trump ya nuna cewa Washington na shirin taka muhimmiyar rawa a abin da zai biyo bayan kama tsohon Shugaban Venezuela Nicolas Maduro da matarsa, Cilia Adela Flores. Trump ya bayyana a wata hira da Fox News cewa Amurka za ta shiga lamarin “cikin sa sosai” domin tabbatar da ‘yanci ga al’ummar Venezuela, tare da jaddada cewa wannan harin na rundunar soji ta musamman ya nuna cewa ba za a rinjayi Amurka ba.
Trump ya kara da cewa Amurka za ta sa hannu sosai a bangaren man fetur na Venezuela, yana mai cewa kasar na da manyan kamfanonin mai a duniya kuma za su taka muhimmiyar rawa a wannan sabon yanayi.
Ya bayyana cewa an kama Maduro ne a wani wuri mai tsaurin tsaro, kuma yanzu yana kan wani jirgin yaki na Amurka, inda ake shirin gurfanar da shi a New York.
Shugaban Amurkan ya tabbatar da cewa babu wani dan Amurka da ya rasu a harin, sai dai ya ce wasu sun yi karamin raunuka amma suna samun sauki. A cewarsa, aikin ya gudana cikin iyakar kulawa, yana mai bayyana cewa ya kalli dukkan matakan harin kamar yana kallon wani shiri na talabijin.














