Isra’ila ta sake buɗe mashigar Rafah tsakanin Gaza da Masar a ranar Litinin domin zirga-zirgar mutane a ƙasa, matakin da zai bai wa Falasɗinawa damar barin yankin tare da dawowar waɗanda suka gudu sakamakon yaƙin Gaza. Wani jami’in tsaron Isra’ila ya ce ƙungiyoyin sa ido na Turai sun isa mashigar, inda aka ba da damar shiga da fita ga mazauna yankin, a cewar Reuters.
Sai dai buɗewar mashigar za ta kasance da ƙuntatawa, inda Isra’ila ta dage kan tsauraran binciken tsaro ga masu shiga da fita. Ana sa ran Isra’ila da Masar za su kayyade adadin matafiya. Isra’ila ta kwace ikon mashigar ne a watan Mayun 2024, kusan watanni tara bayan fara yaƙin Gaza, kafin yarjejeniyar tsagaita wuta ta watan Oktoba da aka cimma da shiga tsakani.
Buɗe Rafah na daga cikin muhimman sharuɗɗan matakin farko na shirin tsagaita wuta, kasancewar rufewar mashigar ta katse babbar hanyar da marasa lafiya da raunana ke bi don neman magani a waje da Gaza. Duk da buɗewar, Isra’ila har yanzu na hana ’yan jarida na ƙasashen waje shiga Gaza, matakin da ƙungiyoyin ’yan jarida ke cewa yana hana samun sahihin bayani.
A halin da ake ciki, shirin tsagaita wuta na gaba ya tanadi mika mulki ga ƙwararrun Falasɗinawa, kwance damarar Hamas da janyewar sojojin Isra’ila yayin sake gina Gaza. Duk da haka, tun bayan yarjejeniyar Oktoba, hare-haren Isra’ila sun kashe sama da Falasɗinawa 500, ciki har da hare-haren sama masu tsanani da aka kai a karshen mako.














