Gabas Ta Tsakiya Filistin Lafiya

Belgium Ta Ce Rushe Ofishin UNRWA a Gabashin Jerusalem Da Isra’ila Ta Yi Ya Saba Wa Dokar Duniya

Belgium ta zargi Isra’ila da karya dokar duniya bayan rushe ofishin UNRWA a Gabashin Jerusalem, tana jaddada cewa mafita daya tilo ita ce kafa kasashe biyu – Isra’ila da Falasdinu.

Newstimehub

Newstimehub

21 Jan, 2026

download 2 8

Gwamnatin Belgium ta bayyana cewa rushe ginin hukumar UNRWA ta Majalisar Dinkin Duniya da Isra’ila ta yi a Gabashin Jerusalem ya sabawa dokar kasa da kasa, tana mai jaddada cewa hanyar zaman lafiya ta gaskiya ita ce kafa kasashe biyu – Isra’ila da Falasdinu.

Ministan harkokin wajen Belgium, Maxime Prévot, ya ce rusa gine-ginen MDD a yankin yana karya dokokin kasa da kasa da kariyar da hukumomin MDD ke da ita. Ya kuma tabbatar da goyon bayan Belgium ga al’ummar Falasdinu, yana cewa suna da hakkin samun zaman lafiya, mutunci da ikon kai wa kansu hukunci. Prévot ya sake jaddada cewa mafita guda daya ita ce two-state solution, wadda za ta bai wa Isra’ila da Falasdinu damar rayuwa cikin zaman lafiya da tsaro.

Ya kuma bayyana damuwa kan tabarbarewar halin jin kai a Gaza da Yammacin Kogin Jordan, yana cewa fadada matsugunan ‘yan share wuri da karuwar tashin hankali na barazana ga duk wani yunkurin samar da zaman lafiya.

Majiyar Labari: AA