Nijeriya Tsaro

Sojojin Najeriya Sun Ceto Tsohon Kanal Ajanaku a Filato Bayan Garkuwa da Shi

Dakarun Najeriya sun kubutar da Kanal Ajanaku mai ritaya a Jihar Filato bayan wani samame na musamman ba tare da biyan kudin fansa ba.

Newstimehub

Newstimehub

6 Jan, 2026

459278870eb746a780260671c2e3fa84d8b820f48b497e29fbff0780271d9a4a

Sojin Najeriya sun samu damar kubutar da Kanal Ajanaku mai ritaya, wanda aka yi garkuwa da shi a karamar hukumar Bassa ta Jihar Filato. Wannan aikin ceto ya faru ne sakamakon gaggawar martanin dakarun da ke gudanar da farmakin “Enduring Peace”.

Rahotanni sun nuna cewa an yi garkuwa da tsohon jami’in ne a safiyar ranar 5 ga Janairu, 2026, da misalin ƙarfe 00:45 na dare daga gidansa da ke kusa da cocin Salvation Army a titin Rukuba. Bayan samun kiran gaggawa, sojojin sashen 1 da 3 tare da hadin gwiwar jami’an leken asiri da yan banga suka bi sahun ‘yan bindigar zuwa yankin Wildlife Park inda suka fara bincike mai zurfi.

Takaitaccen lokaci bayan haka, masu garkuwar sun tuntubi iyalinsa inda suka nemi fansar Naira miliyan 200 tare da barazanar kashe shi saboda tsananin matsin lambar sojojin. Don kauce wa hatsari, dakarun suka koma aiki a ɓoye, wanda daga bisani ya kai ga nasarar kubutar da shi da misalin ƙarfe 17:30 na ranan nan a Rafiki Axis, Bassa, ba tare da an biya fansa ba.

Rundunar sojin ta tabbatar da cewa lafiyar Kanal Ajanaku tana da kyau, kuma yana ci gaba da samun kulawar likitoci. Haka kuma, ana ci gaba da farautar ‘yan bindigar tare da wargaza maboyarsu domin tabbatar da tsaro a yankin.

Rundunar sojin Najeriya ta sake nanata kudirinta na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da hana masu aikata laifuka damar yin barna a yankin.

Majiyar Labari: TRT HAUSA