Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana cewa sabon “Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza” wata dama ce ta tarihi da za ta iya samar da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin, tare da kawo ƙarshen dogon wahala da al’ummar Falasɗinu ke fuskanta.
A wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Fidan ya ce kwamitin – wanda Shugaba Recep Tayyip Erdogan yake daga cikin waɗanda suka kafa shi – zai taimaka wajen biyan buƙatun jin ƙai na Gaza, tare da shimfiɗa tubalin zaman lafiya mai adalci da haɗa kowa da kowa.
Fidan ya bayyana cewa ya halarci bikin sanya hannu kan Yarjejeniyar Kwamitin Zaman Lafiya na Gaza a Davos, Switzerland, a madadin Shugaba Erdogan.
“Mun yi imani cewa ta hanyar aiki kafada da kafada da mutanen Gaza, wannan kwamiti zai taka muhimmiyar rawa wajen gina makomar Gaza, taimaka wa yankin ya farfaɗo, da kuma ba da damar zaman lafiya ya samu tushe,” in ji shi.
Ministan ya kuma jaddada matsayin Turkiyya cewa akwai makomar da za a ji muryar al’ummar Gaza, a kare haƙƙoƙinsu, kuma su rayu cikin zaman lafiya da mutunci.
Fadar White House ta sanar da kafa wannan kwamiti a makon da ya gabata, tare da amincewa da Kwamitin Kasa na Gudanar da Gaza, wanda ke cikin hukumomi huɗu da za su kula da matakin sauyin mulki a yankin.
Wannan shiri yana cikin wani tsari na maki 20 da Shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar, wanda Kwamitin Tsaron Majalisar Ɗinkin Duniya ya amince da shi ƙarƙashin kuduri na 2803 a watan Nuwamba da ya gabata.














