Hukumar Ghana Education Service (GES) ta bayyana cewa Juma’a, 23 ga Janairu, 2026, za a rika bikin ta a faɗin ƙasar a matsayin Ranar Ci Gaban Kwarewa ta Ƙasa (National Continuous Professional Development – CPD Day) ga malamai.
A cikin wata sanarwa da GES ta fitar a ranar Laraba, 15 ga Janairu, hukumar ta ce matakin na nuni da muhimmancin horaswa da sabunta kwarewar malamai domin inganta koyarwa da ƙarfafa ƙwarewar masu ilimi a ƙasar.
GES ta ce an ware ranar CPD ne domin bai wa malamai cikakken goyon bayan hukuma da isasshen lokaci ba tare da katsalandan ba, domin halartar mataki na biyu na shirin horaswa kan tsaron yanar gizo da kare bayanai (Cybersecurity and Data Protection).
Domin tabbatar da cewa malamai sun samu damar mayar da hankali kan horaswar gaba ɗaya, hukumar ta kuma ayyana ranar 23 ga Janairu, 2026 a matsayin hutu ga ɗalibai, domin kada ayyukan koyarwa su kawo cikas ga shirin.
Hukumar ta umarci dukkan Daraktocin Ilimi na Jihohi (Regions) da su isar da sanarwar ga Daraktocin Kananan Hukumomi da na Gundumomi, tare da shugabannin makarantun firamare da sakandare, domin a tabbatar da cikakken bin umarnin.
GES ta kammala da kira ga dukkan hukumomin makarantu da su ba da haɗin kai yadda aka saba domin nasarar aiwatar da Ranar CPD ta malamai a faɗin Ghana.














