Harin sama da Isra’ila ta kai a kusa da birnin Tyre ya kashe mutum guda tare da jikkata wasu biyu, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cim ma tun watan Nuwamban 2024, lamarin da ya sake tayar da hankula game da tabarbarewar tsaro a yankin.
Ma’aikatar Lafiya ta Lebanon ta tabbatar da cewa jirgin yaki marar matuki ya kai hari kan wata mota a wajen Tyre, wanda daga bisani kungiyar Hezbollah ta ce dan jaridar gidan talabijin na Al-Manar, Ali Nour Al-Din, ne ya rasa ransa.
Har ila yau, jiragen Isra’ila sun rika shawagi a sararin samaniyar Zahrani da Bisariyeh, inda aka jefa bama-bamai a kan masana’anta da gidaje a yankunan Aitaroun da Hreika.
Rahotanni sun nuna cewa tankokin Isra’ila sun kai farmaki daga sabon sansanin soji da suka kafa a Jabal Al-Bat, yayin da har yanzu suke ci gaba da mamaye kudancin Lebanon, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta. Tun daga Oktoban 2023 zuwa Satumba 2024, hare-haren Isra’ila sun yi sanadiyyar mutuwar fiye da mutane 4,000 a Lebanon.














