Ministan Tsaron Ƙasa na Isra’ila mai tsananin ra’ayi, Itamar Ben-Gvir, ya nuna goyon bayansa ga wani kudirin doka da ke neman hana kiran sallah a masallatai, inda ya ce kiran yana “damun” Yahudawa a wuraren zama.
Kudirin dokar, wanda jam’iyyarsa Jewish Power ta gabatar, yana buƙatar kowanne masallaci ya nemi izinin gwamnati kafin yin kiran sallah, tare da bin wasu sharudda da suka haɗa da rage ƙarar makirufo, duba wurin da masallaci yake da kuma kusancinsa da unguwannin zama.
Falasɗinawa da ke Isra’ila sun yi Allah wadai da shirin, suna cewa matakin na ƙara kai hari ne ga ‘yancinsu na addini da kuma asalinsu.
A ƙarƙashin kudirin, jami’an ’yan sanda za su sami ikon rufe ko kwace lasifikocin masallatai nan take. Har ila yau, an tanadi manyan tarar kuɗi: Shekel 50,000 (kus. $15,660) idan aka yi amfani da makirufo ba tare da izini ba, da Shekel 10,000 (kus. $3,100) idan aka karya sharuddan izinin.
Irin wannan kudiri ya taɓa wucewa a 2017, amma bai taɓa kafuwa da cikakken aiki ba.














