Nijeriya

NCC Ta Gargaɗi Masu Gini Kan Lalata Layukan Sadarwa na Ƙarƙashin Ƙasa a Nijeriya

Hukumar NCC tare da NSCDC sun gargadi masu aikin gini da hanyoyi cewa lalata layukan fibre-optic laifi ne da zai iya kai su gaban kotu.

Newstimehub

Newstimehub

5 Feb, 2026

f326655d34f84ad747545de93074ff41c5fc1a8157da07b53fe0dc71c1f0a206

A ƙoƙarin kare muhimman kayayyakin sadarwa na ƙasa, Hukumar Kula da Sadarwa ta Nijeriya (NCC) tare da Hukumar Kare Farar-Hula (NSCDC) sun ja kunnen kamfanonin gine-gine da masu aikin hanya kan yawaitar lalata layukan sadarwa na ƙarƙashin ƙasa. Hukumomin sun bayyana cewa wannan matsala na faruwa ne sakamakon sakaci, kuma ba za a ƙara lamunta ba.

NCC da NSCDC sun ce lalata layukan fibre-optic laifi ne a ƙarƙashin dokar Critical National Information Infrastructure (CNII) Order 2024, inda aka ayyana su a matsayin muhimman kayayyakin sadarwa na ƙasa. Sun yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifi—ko mutum ɗaya, kamfani ko ɗan kwangilar gwamnati—zai fuskanci hukunci a kotu, saboda illar da hakan ke yi ga tsaron ƙasa, tattalin arziki da lafiyar jama’a.

Majiyar Laari: TRT HAUSA