Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargaɗi cewa wasu jihohin arewacin ƙasar na fuskantar ƙarin haɗarin kamuwa da cutar sankarau yayin da yanayin zafi ke ƙaruwa. Hukumar ta bayyana cewa cutar sankarau na shafar ƙwayoyin kariya da ke rufe ƙwaƙwalwa da lakar baya, kuma galibi ƙwayar cuta Neisseria meningitidis ce ke haddasa ta.
NiMet ta ce cutar na yaɗuwa ta hanyar numfashi daga mutum zuwa mutum, musamman a wuraren da ake cunkoso ko inda iska ba ta shiga sosai. Jihohin da aka fi ganin suna cikin haɗari sun haɗa da Sokoto, Zamfara, Kebbi, Katsina, Kano, Jigawa, Adamawa, Gombe, Bauchi, Yobe da Borno.
Hukumar ta buƙaci mazauna yankunan tsakiyar ƙasar su kasance cikin lura da alamomin cutar tare da kai rahoton duk wani zargi da wuri. Jihohin Filato, Oyo, Cross River, Edo, Ekiti da Enugu kuma an sanya su cikin yankunan da ake sa ido a kansu.
NiMet ta jaddada cewa gano cutar da wuri da kuma yin rigakafi na iya ceton rayuka, musamman ga yara da matasa da kuma mutanen da ke rayuwa a wuraren cunkoso. Alamomin cutar sun haɗa da zazzabi mai tsanani, matsanancin ciwon kai, wuya mai tauri, tashin zuciya ko amai, da kuma jin haske yana damun ido.
Majiyar Labari: Trt Hausa














