Kwallon kafa a Afirka na ci gaba da kasancewa ƙarƙashin jagorancin manyan ƙasashe na Arewa da Yammacin Afirka, kamar yadda sabon jadawalin FIFA Men’s World Rankings ya nuna. Duk da sauye-sauyen da ke faruwa lokaci zuwa lokaci, manyan ƙungiyoyin nahiyar sun ci gaba da riƙe matsayinsu, suna nuna ƙarfin su a fagen duniya yayin da shekarar 2025 ta ƙare kuma 2026 ta fara.
A cewar sabon rahoton FIFA, waɗannan su ne manyan ƙungiyoyi 7 na Afirka a halin yanzu:
Senegal
Morocco
Najeriya
Algeria
Masar (Egypt)
Ivory Coast (Côte d’Ivoire)
DR Congo
Waɗannan ƙasashe sun dade suna nuna ƙwarewa a gasannin nahiyar da na duniya, musamman a AFCON da kuma cancantar shiga gasar cin kofin duniya, lamarin da ya tabbatar da su a matsayin ginshiƙan ƙwallon kafa na Afirka.
Najeriya, wacce ta hau matsayi na 26 a duniya, ta ci gaba da zama cikin manyan ƙasashe uku a Afirka, yayin da Senegal da Morocco ke fafatawa a saman tebur bayan nasarorinsu a AFCON da sauran manyan wasanni.














